• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tinubu Ba Za Ta Goyi Bayan Auren Jinsi Ba – Minista 

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Yajin aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ba za ta goyi bayan duk wani yunƙuri na auren jinsi ko tarayyar ‘yan luwaɗi da maɗigo a Nijeriya ba.

Ministan ya bayyana haka ne a yayin da yake martani kan labarin da aka yaɗa a ranar Alhamis cewa Gwamnatin Tarayya ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da aka yi a ƙasar Samoa, wadda za ta ba da dama a hukumance ga ‘yan luwaɗi da masu maɗigo a Nijeriya.

  • Huldar Abotar Dindindin Tsakanin Sin Da Kazakhstan Na Samun Ci Gaba Zuwa Sabon Mataki
  • An Fitar Da Alkaluman Awon Yadda Ake Hade Ayyukan Masana’antu Da Fasahar AI A Sin

A rahoton da wasu kafafen yaɗa labarai suka buga, an ruwaito cewa, yarjejeniyar ta ƙunshi wasu tanade-tanade ne waɗanda ke buƙatar goyon bayan kare haƙƙin ‘yan luwaɗi da masu maɗigo a matsayin sharaɗin samun tallafin kuɗi da sauran taimako daga ƙasashen da suka ci gaba.

Lamarin dai ya haifar da ce-ce-ku-ce, inda wasu malaman addini da masu rajin kare haƙƙin ɗan Adam ke sukar gwamnati kan amincewa da yarjejeniyar da ta yi.

To amma a ƙarin hasken da ya yi kan yarjejeniyar, Minista Idris ya ce ai Nijeriya tana da dokoki tun tuni waɗanda suka haramta auren jinsi ko tarayyar ‘yan luwaɗi da masu maɗigo, kuma dokokin sun girmi wannan yarjejeniyar ta Samoa da ake ta ce-ce-ku-ce a kan ta.

Labarai Masu Nasaba

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

Ya ce, “A ranar 28 ga Yuni, 2024 ne gwamnatin Nijeriya ta rattaba hannu kan yarjejeniyar Samoa ɗin a sakatariyar Ƙungiyar Ƙasashen Afirka, Karibbiyan da Pacific (OACPS) a birnin Brussels na ƙasar Beljiyam.

“An fara tattaunawa kan yarjejeniyar tun a shekarar 2018, a lokacin taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 73. Ɗaukacin ƙasashe membobin Tarayyar Turai su 27 da ƙasashe 47 daga cikin 79 na OACPS ne suka rattaba hannu kan yarjejeniyar a garin Apia da ke Tsibirin Samoa a ranar 15 ga Nuwamba, 2018.

“Nijeriya ta rattaba hannu kan yarjejeniyar ne a ranar Juma’a, 28 ga Yuni, 2024. Hakan ya biyo bayan nazarin da ta yi tare da tuntuɓar Kwamitin Ministoci da Ma’aikatar Kasafin Kuɗi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki ta kafa tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Harkokin Ƙasashen Waje da Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya.

“An tabbatar da cewa babu ɗaya daga cikin Tanade-tanade 103 na yarjejeniyar waɗanda suka saɓa wa Kundin Tsarin Mulki na 1999 wanda aka yi wa kwaskwarima ko dokokin Nijeriya, da sauran wasu dokoki.

“Bugu da ƙari, amincewar da Nijeriya ta yi yana ƙunshe da sanarwa mai ɗauke da kwanan wata 26 ga Yuni, 2024, inda ta fayyace fahimtar ta da kuma yanayin yarjejeniyar a ƙarƙashin ikon ta na cewa ba a amince da duk wani tanadi da ya saɓa wa dokokin Nijeriya ba.

“Yana da kyau a lura da cewa akwai dokar da aka kafa a Nijeriya game da dangantakar auren jinsi ɗaya tun a cikin 2014.”

A ƙarshe, ministan ya ce, “Ya zama wajibi a tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, kasancewar ta gwamnati mai bin ƙa’ida, ba za ta shiga wata yarjejeniya ta ƙasa da ƙasa wadda za ta cutar da ƙasa da ‘yan ƙasar ta ba.

“Yarjejeniyar Samoa ba komai ba ce illa wani muhimmin tsarin doka na haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen ƙungiyar OACPS da Tarayyar Turai don inganta cigaba mai ɗorewa, da yaƙi da sauyin yanayi da illolinsa, da samar da damar zuba jari, da samar da haɗin gwiwa tsakanin ƙasashe mambobin OACPS a matakin ƙasa da ƙasa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LuwadiMaɗigoSamoaTarayyar Turai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fifikon Manzon Allah (SAW): Darasi Daga Suratun Najmi (1)

Next Post

An Aike Ɗan Shekara 67 Gidan Yari Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Mata 2 Fyaɗe Yana Ba Su ₦500 A Bauchi

Related

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
Labarai

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

1 minute ago
Neja
Labarai

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

1 hour ago
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Labarai

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

1 hour ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

3 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

5 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

6 hours ago
Next Post
An Aike Ɗan Shekara 67 Gidan Yari Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Mata 2 Fyaɗe Yana Ba Su ₦500 A Bauchi

An Aike Ɗan Shekara 67 Gidan Yari Kan Zargin Yi Wa 'Yan Mata 2 Fyaɗe Yana Ba Su ₦500 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

September 15, 2025
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

September 15, 2025
Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

September 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.