• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tinubu Ta Ba ‘Yan Jarida Cikakken ‘Yanci – Minista

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tinubu Ta Ba ‘Yan Jarida Cikakken ‘Yanci – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya tabbatar da cewa babu wani ɗan jarida ɗaya da aka kama ko aka ɗaure a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu saboda gudanar da aikin jarida yadda ya kamata.

Ya jaddada cewa kafafen yaɗa labarai suna da cikakken ‘yanci a Nijeriya.

  • Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (6)
  • Yadda Za Ki Ja Hankalin Miji A Lokacin Da Ba Shi Da Sha’awa

Idris ya faɗi haka ne a yayin da ya ke amsa wata tambaya a wani taron manema labarai da ma’aikatar sa ta shirya tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Kula Da Muhalli ta Tarayya da kuma Hukumar Ilimi da Kimiyya ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNESCO), domin tunawa da Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida ta Duniya ta bana wanda aka yi a Abuja ranar Juma’a.

Ya ce: “A zamanin wannan gwamnatin, a misali, ban ga wani mutum wanda aka ɗaure ko kuma ya yi gudun hijira sakamakon ‘yancin aikin jarida ba.

“Mun san abin da ya faru a ƙasar nan a baya. A wasu shekarun da suka gabata, mun san cewa dole ne ku bar ƙasar nan don samun damar ba da rahoto. Zan iya gaya muku cewa ‘yan jarida a Nijeriya suna da ‘yanci amma za a iya ƙarfafa ‘yancin ne idan aka tabbatar da gaskiya ta hanyar da muke kawo rahoto.”

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

Ministan ya ce Shugaban Ƙasa Tinubu ya fahimci muhimmancin yaɗa labarai yadda ya kamata wajen wayar da kai, faɗakarwa, da ilimantar da ‘yan Nijeriya da duniya baki ɗaya, inda ya ƙara da cewa ta hanyar ba da sahihan bayanai a kan lokaci za a iya faɗakar da kowa sosai, kuma kafafen yaɗa labarai na iya zama makami mai ƙima na bunƙasa gaskiya da riƙon amana.

“A matsayin mu na Ma’aikata da Gwamnati, mun ba da dama ga ‘yan jarida ba tare da wata matsala ba kuma mun samar da yanayi mai dacewa wanda ya ci gaba da ƙarfafa wa kafafen yaɗa labarai na Nijeriya ƙwarin gwiwa don bunƙasa,” inji shi.

Ministan ya tunatar da kafafen yaɗa labarai cewa yaɗa labarin ƙarya bai dace da aikin jarida ba kuma ba za a iya kwatanta shi da ‘yancin jarida ba.

Ya ce yayin da Shugaba Tinubu ke ƙoƙarin ganin Nijeriya ta zama wata ƙasa mai jan hankali wajen zuba jari kai-tsaye daga ƙasashen waje, dole ne kafafen yaɗa labarai su gabatar da kyakkyawan bayanin ƙasar ga ƙasashen duniya.

Yayin da ya ke magana kan taken Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida ta Duniya na bana, wato ”Jarida ta Duniya: Aikin Jarida a yayin da ake fuskantar Matsalar Muhalli,” Idris ya ce duniya na fuskantar matsalar muhalli mai girman gaske wanda ba a taɓa ganin irin sa ba, wanda ke haifar da barazana ba kawai ga duniya ba amma ga makomar bil’adama.

Ya ce sauyin yanayi, asarar rabe-raben halittu, gurɓacewar yanayi, da ƙarewar albarkatu munanan abubuwa ne da ke buƙatar ɗaukar matakin gaggawa kan wayar da kan jama’a.

Ya ce, “Mu yi imani da cewa ‘yancin ‘yan jarida ba wai kawai haƙƙin ɗan’adam ba ne; ya na da muhimmanci don ɗorewar muhalli. Idan babu ‘yan jarida masu ‘yanci da zaman kan su, ba za mu iya fatan magance matsalolin muhalli da mu ke fuskanta ba.

“Yaɗa labaran ƙarya yana lalata fahimtar jama’a game da matsalolin muhalli kuma yana hana mu damar ɗaukar matakai masu ma’ana.

“Don haka dole ne mu tsaya tsayin daka wajen kare ‘yancin ‘yan jarida tare da tallafa wa ayyukan ‘yan jarida masu sadaukar da kai wajen bayar da labarin gaskiya.”

Taron ya samu halartar Ƙaramin Ministan Kula da Muhalli, Dakta Iziaq Adekunle Salako; Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Mista Bayo Onanuga; Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Watsa Labarai Da Wayar Da Kai, Dakta Ngozi Onwudiwe; Shugaban Ofishin UNESCO na Abuja, Mista Abdourahamane Diallo, da shugabannin hukumomin Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai da kuma Ma’aikatar Kula da Muhalli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TinubuMinistan yada labaraiNUJ
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanoni 530 Suka Nuna Bukatar Neman Aikin Gyaran Jiragen Kasan Nijeriya Na Naira Biliyan 11

Next Post

Idan Mace Ta Yi Barin Cikin Wata Biyu, Za Ta Dakatar Da Yin Sallah?

Related

Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

8 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

9 hours ago
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu
Labarai

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

10 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

11 hours ago
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

11 hours ago
Muddin Nahiyar Afirka Ta Farka Ba Za A Iya Raina Ta Ba
Labarai

Yara 400,000 Ne Ke Kamuwa Da Cutar Kansa Duk Shekara A Duniya

11 hours ago
Next Post
Idan Mace Ta Yi Barin Cikin Wata Biyu, Za Ta Dakatar Da Yin Sallah?

Idan Mace Ta Yi Barin Cikin Wata Biyu, Za Ta Dakatar Da Yin Sallah?

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.