• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tinubu Ta Ba ‘Yan Jarida Cikakken ‘Yanci – Minista

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tinubu Ta Ba ‘Yan Jarida Cikakken ‘Yanci – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya tabbatar da cewa babu wani ɗan jarida ɗaya da aka kama ko aka ɗaure a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu saboda gudanar da aikin jarida yadda ya kamata.

Ya jaddada cewa kafafen yaɗa labarai suna da cikakken ‘yanci a Nijeriya.

  • Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (6)
  • Yadda Za Ki Ja Hankalin Miji A Lokacin Da Ba Shi Da Sha’awa

Idris ya faɗi haka ne a yayin da ya ke amsa wata tambaya a wani taron manema labarai da ma’aikatar sa ta shirya tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Kula Da Muhalli ta Tarayya da kuma Hukumar Ilimi da Kimiyya ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNESCO), domin tunawa da Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida ta Duniya ta bana wanda aka yi a Abuja ranar Juma’a.

Ya ce: “A zamanin wannan gwamnatin, a misali, ban ga wani mutum wanda aka ɗaure ko kuma ya yi gudun hijira sakamakon ‘yancin aikin jarida ba.

“Mun san abin da ya faru a ƙasar nan a baya. A wasu shekarun da suka gabata, mun san cewa dole ne ku bar ƙasar nan don samun damar ba da rahoto. Zan iya gaya muku cewa ‘yan jarida a Nijeriya suna da ‘yanci amma za a iya ƙarfafa ‘yancin ne idan aka tabbatar da gaskiya ta hanyar da muke kawo rahoto.”

Labarai Masu Nasaba

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Ministan ya ce Shugaban Ƙasa Tinubu ya fahimci muhimmancin yaɗa labarai yadda ya kamata wajen wayar da kai, faɗakarwa, da ilimantar da ‘yan Nijeriya da duniya baki ɗaya, inda ya ƙara da cewa ta hanyar ba da sahihan bayanai a kan lokaci za a iya faɗakar da kowa sosai, kuma kafafen yaɗa labarai na iya zama makami mai ƙima na bunƙasa gaskiya da riƙon amana.

“A matsayin mu na Ma’aikata da Gwamnati, mun ba da dama ga ‘yan jarida ba tare da wata matsala ba kuma mun samar da yanayi mai dacewa wanda ya ci gaba da ƙarfafa wa kafafen yaɗa labarai na Nijeriya ƙwarin gwiwa don bunƙasa,” inji shi.

Ministan ya tunatar da kafafen yaɗa labarai cewa yaɗa labarin ƙarya bai dace da aikin jarida ba kuma ba za a iya kwatanta shi da ‘yancin jarida ba.

Ya ce yayin da Shugaba Tinubu ke ƙoƙarin ganin Nijeriya ta zama wata ƙasa mai jan hankali wajen zuba jari kai-tsaye daga ƙasashen waje, dole ne kafafen yaɗa labarai su gabatar da kyakkyawan bayanin ƙasar ga ƙasashen duniya.

Yayin da ya ke magana kan taken Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida ta Duniya na bana, wato ”Jarida ta Duniya: Aikin Jarida a yayin da ake fuskantar Matsalar Muhalli,” Idris ya ce duniya na fuskantar matsalar muhalli mai girman gaske wanda ba a taɓa ganin irin sa ba, wanda ke haifar da barazana ba kawai ga duniya ba amma ga makomar bil’adama.

Ya ce sauyin yanayi, asarar rabe-raben halittu, gurɓacewar yanayi, da ƙarewar albarkatu munanan abubuwa ne da ke buƙatar ɗaukar matakin gaggawa kan wayar da kan jama’a.

Ya ce, “Mu yi imani da cewa ‘yancin ‘yan jarida ba wai kawai haƙƙin ɗan’adam ba ne; ya na da muhimmanci don ɗorewar muhalli. Idan babu ‘yan jarida masu ‘yanci da zaman kan su, ba za mu iya fatan magance matsalolin muhalli da mu ke fuskanta ba.

“Yaɗa labaran ƙarya yana lalata fahimtar jama’a game da matsalolin muhalli kuma yana hana mu damar ɗaukar matakai masu ma’ana.

“Don haka dole ne mu tsaya tsayin daka wajen kare ‘yancin ‘yan jarida tare da tallafa wa ayyukan ‘yan jarida masu sadaukar da kai wajen bayar da labarin gaskiya.”

Taron ya samu halartar Ƙaramin Ministan Kula da Muhalli, Dakta Iziaq Adekunle Salako; Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Mista Bayo Onanuga; Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Watsa Labarai Da Wayar Da Kai, Dakta Ngozi Onwudiwe; Shugaban Ofishin UNESCO na Abuja, Mista Abdourahamane Diallo, da shugabannin hukumomin Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai da kuma Ma’aikatar Kula da Muhalli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TinubuMinistan yada labaraiNUJ
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanoni 530 Suka Nuna Bukatar Neman Aikin Gyaran Jiragen Kasan Nijeriya Na Naira Biliyan 11

Next Post

Idan Mace Ta Yi Barin Cikin Wata Biyu, Za Ta Dakatar Da Yin Sallah?

Related

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri
Labarai

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

7 minutes ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

1 hour ago
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
Labarai

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

3 hours ago
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 
Labarai

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

4 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

12 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

13 hours ago
Next Post
Idan Mace Ta Yi Barin Cikin Wata Biyu, Za Ta Dakatar Da Yin Sallah?

Idan Mace Ta Yi Barin Cikin Wata Biyu, Za Ta Dakatar Da Yin Sallah?

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

June 27, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.