ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tinubu Ta Fito Da Tsare-tsaren Bunƙasa Tattalin Arziki Da Samar Da Ayyukan Yi

by Sulaiman
2 years ago
Tinubu

Gwamnatin Tarayya ta fito da wasu tsare-tsare waɗanda za su taimaka wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar nan tare da samar da aikin yi.

Ministar Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Dakta Doris Uzoka-Anite, ita ce ta bayyana haka a wurin wani taro na musamman da ‘yan jarida wanda Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, a ƙarƙashin minista Alhaji Mohammed Idris, ta shirya a ranar Juma’a a Cibiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa da ke Abuja.

  • Durƙushewar Darajar Naira: Atiku Ya Ba Da Mafita Bayan Ya Caccaki Tinubu
  • Dennis Francis: Bikin Bazara Kyauta Ce Da Kasar Sin Ta Baiwa Duniya

Taron shi ne na biyu a ci gaba da jagorantar ministoci da Idris ke yi domin su riƙa bayyana wa manema labarai irin ci gaban da suka samar a watanni shida da su ka yi, sai kuma bayyana musu irin alƙiblar da ake fuskanta nan gaba.

ADVERTISEMENT

Tun da farko, Ministan yada labarai, Idris ya buɗe taron da jawabi inda ya ce: “Mun taru a nan domin gina ginshiƙin yarda, amana a tsakaninmu da ‘yan jarida, ta yadda za mu tabbatar cewa, ana sanarwa jama’a abin da muke aiwatarwa.

“Wannan taro ya ba ku damar ku gana kai-tsaye da manyan jami’an gwamnati, ku yi mana tambayoyin da suka cancanta da waɗanda suka shige wa jama’a a duhu.”

LABARAI MASU NASABA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

Ministan ya jaddada ƙoƙarin da ma’aikatarsa ke yi wajen yin komai a fili ba tare da ƙumbiya-ƙumbiya ba.

Ya nanata damar samun bayanai da manema labarai ɗin ke da ita, tare da bayyana muhimmiyar rawar da ‘yan jarida ke takawa wajen isar da saƙonni ga jama’a.

Haka kuma ya ƙara nuna ƙoƙarin tabbatar da yaɗa labarai a kusa da nesa, ta hanyar da aka saba da kuma sabbin hanyoyin na’urorin zamani masu kai saƙonni nesa, nan take.

Yayin da ta ke nata jawabin ga manema labaran, Dakta Doris Uzoka-Anite ta zayyana shirye-shiryen bunƙasa tattalin arzikin da ta bijiro da su, waɗanda ta ce, har samar da ɗimbin ayyukan yi ga ɗimbin ‘yan Nijeriya za su yi.

Ta ce dukkan waɗannan shirye-shirye sun ta’allaƙa ne bisa turbar shikashikai takwas na Shirin Shugaban Ƙasa na Fata Nagari, wanda a Turance ake kira ‘Renewed Hope,’ waɗanda su ka haɗa da bunƙasa tattalin arzikin ƙasa, samar da ayyukan yi, samar da jari, samar da yanayin gudanar da kasuwanci mai yalwa, rage fatara da talauci.

Ministar ta ce ma’aikatar ta na nan ta na tattauna yadda Nijeriya za ta samu damar cin gajiyar tsarin gudanar da cinikayya a sauƙaƙe tsakanin ƙasashen Afirka, wato AFCFTA.

Ta ce gudanar da wannan kasuwanci kai-tsaye ba tare da tarnaƙi ba zai faɗaɗa kasuwanci tsakanin ƙasashen Afirka, kuma zai ƙara ba da damar shigowar masu zuba jari.

Ta ce a taron baya-bayan nan na 13 na Ministocin Kasuwanci da Cinikayya na AFCFTA, an jaddada matsayin da Nijeriya ke da shi wajen bunƙasar kasuwanci ta hanyar fasahar zamani, sai kuma ƙoƙarin da ƙasar ke yi wajen daƙile haramtaccen ciniki ta hanyar amfani da jiragen ruwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,
Kasashen Ketare

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Next Post
Adadin Sayayya Ta Yanar Gizo Ta Karu Yayin Hutun Bikin Bazara Na Kasar Sin

Adadin Sayayya Ta Yanar Gizo Ta Karu Yayin Hutun Bikin Bazara Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.