• Leadership Hausa
Sunday, June 4, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Yobe Za Ta Bai Wa Malamai Bashin Noma Kimanin Naira Miliyan 500

by Muhammad Maitela
3 months ago
in Labarai
0
Gwamnatin Yobe Za Ta Bai Wa Malamai Bashin Noma Kimanin Naira Miliyan 500
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Yobe Mai Mala Buni, ya amince da bai wa Malaman makaranta akalla 4,000 bashin Naira miliyan 500 domin bunkasa harkokin noma a fadin jihar.

Gwamnan ya sanar da hakan a sanarwar manema labaru, mai dauke da sa-hannun Darakta Janar kan hulda da yan jaridu da kafafen yada labaru, Alhaji Mamman Mohammed, inda ya kara da cewa, za a bayar da bashin kan hanyoyi biyu; domin inganta jindadin malaman tare da daura damarar shiga daminar wannan shekara ta 2023.

  • Dan Sanda Ya Harbe Kansa Da Budurwarsa A Kwara
  • Wani Bikin Kaddamarwa Mai Muhimmanci

Alhaji Mamman ya kara da cewa, kowane daya daga cikin wannan adadi na malamai 4,000 zai karfi kimanin naira 120,000 wajen shiga harkar noman don bunkasa jihar da abinci.

Bugu da kari kuma, Gwamna Buni ya shawarci wadanda za su ci gajiyar kudin su yi amfani da tallafin ta hanyar da ya dace, kuma bisa manufar da aka basu bashin.

Sanarwar ta kara da bayyana cewa, bashin zai gudana ne a karkashin bankin ‘Yobe Microfinance’ tare da biyan sa cikin watanni 24 (shekara biyu) ta hanyar Ma’aikatar kudi da Ma’aikatar Kananan hukumomi da harkokin masarautu na jihar Yobe.

Labarai Masu Nasaba

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

A nashi bangaren, Manajan Darakta a Bankin Yobe Microfinance, Dr. Sheriff Al-Muhajir, ya bayyana cewa shirye-shiryen aiwatar da raba kudin ya kankama a matakin karshe, wanda kuma nan da lokaci kadan za a fara raba kudin kafin shigar damina.

“Yanzu haka muna aiki a matakin karshe na shirye-shiryen aiwatar da bayar da bashin.”

“Sannan zan kara da sanar da cewa, makasudin Mai Girma Gwamna Mai Mala Buni kan wannan shirin, shi ne wadanda zasu ci gajiyar wannan bashin, za su yi amfani da bashin wajen yin noma domin bunkasa samar da abinci.” In ji Al-Muhajir.

Tags: BashiManomaYobe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Sanda Ya Harbe Kansa Da Budurwarsa A Kwara

Next Post

Sin Ta Taya Murnar Bola Tinubu Ya Zama Shugaban Nijeriya

Related

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 
Labarai

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

47 mins ago
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

2 hours ago
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli
Labarai

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

5 hours ago
Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano
Manyan Labarai

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

6 hours ago
Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu
Manyan Labarai

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

11 hours ago
Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo
Labarai

Babu Gaskiya A Labarin Mutuwar Akeredolu -Gwamnatin Ondo

21 hours ago
Next Post
Sin Ta Taya Murnar Bola Tinubu Ya Zama Shugaban Nijeriya

Sin Ta Taya Murnar Bola Tinubu Ya Zama Shugaban Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

June 4, 2023
Tawagar Sojin Injiniya Ta Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Kasar Sin Ta Tallafawa Kongo Kinshasa Ta Fuskar Aikin Ceto

Tawagar Sojin Injiniya Ta Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Kasar Sin Ta Tallafawa Kongo Kinshasa Ta Fuskar Aikin Ceto

June 4, 2023
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

June 4, 2023
Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

June 4, 2023
Sana’ar Kwalliya

Sana’ar Kwalliya

June 4, 2023
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

June 4, 2023
Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

June 4, 2023
Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

June 4, 2023
Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

June 4, 2023
Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

June 4, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.