• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Bada Umurnin Ɗaukar ‘Yan Sa-kai

Za Ta Gina Tare Da Sabunta Azuzuwa Sama Da 200

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai
0
Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Litinin ne gwamna Dauda Lawal ya bayar da umurnin ɗaukar ‘yan sa-kai a matsayin ƙari ga ƙoƙarin da jami’an tsaro ke yi don magance matsalar tsaro.

Ɗaukar ‘yan sa-kai na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da aka tattauna a zaman majalisar zartaswar jihar Zamfara, wanda Gwamna Lawal ɗin ya jagoranta.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Rufe Wasu Kasuwannin Shanu A Jihar

Wata sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta ce an gudanar da wannan zama na majalisar zartaswar ne a fadar gwamnatin jihar dake Gusau.

Ya ƙara da cewa, har wayau, a wurin taron majalisar ta bada umurnin a gina sabbin azuzuwan karatu, tare da sabunta wasu a faɗin ƙananan hukumomi 14 na Jihar.

Ya ce: “A yunƙurinsa na ganin an kawo ƙarshen matsalar tsaro, Gwamna Dauda Lawal ya aminta da ɗaukar ‘yan sa-kai a dukkanin ƙananan hukumomin Zamfara.

Labarai Masu Nasaba

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

“Duk dai a zaman majalisar zartaswar da ya jagoranta, ya aminta da ginawa, tare da sabunta azuzuwan karatu a faɗin ƙananan hukumomin.

“Za a ɗauki ‘yan sa-kai 300 a kowacce ƙaramar hukuma ta jihar. Waɗanda za a basu horaswar da ta dace, domin su ci gaba da taimakawa soji da ‘yan sanda kan yaƙi da ‘yan ta’adda.

“Majalisar ta aminta da gina sabbi tare da sabunta azuzuwan karatu guda 49 a Gusau, 11 a Anka, 15 a Bakura, 8 a Bukkuyum, 14 a Birnin Magaji, 8 a Bungudu, 8 a Gummi, 19 a Kauran Namoda, 8 a Maru, 11 a Maradun, 42 a Shinkafi, 8 a Talata Mafara, 27 a Tsafe da kuma guda 11 a Zurmi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Sa-KaiTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Za A Dora Wa Laifin Matsalar Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba – Sanusi

Next Post

Kamfanin Makamashi Na Sin Ya Cimma Gagarumar Nasara A Fannin Karfin Wutar Lantarki Da Ake Iya Sabuntawa

Related

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

42 minutes ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

2 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

2 hours ago
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano
Labarai

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

3 hours ago
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

6 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

7 hours ago
Next Post
Kamfanin Makamashi Na Sin Ya Cimma Gagarumar Nasara A Fannin Karfin Wutar Lantarki Da Ake Iya Sabuntawa

Kamfanin Makamashi Na Sin Ya Cimma Gagarumar Nasara A Fannin Karfin Wutar Lantarki Da Ake Iya Sabuntawa

LABARAI MASU NASABA

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.