• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnoni Sun Ta Ya Musulmin Nijeriya Murnar Sallah Babba

byAbubakar Abba
2 years ago
Sallah

Wasu daga cikin gwamnonin kasar nan, sun bukaci daukacin Musulmi da su yi amfani da lokutan Sallah wajen yin addu’oin samun zaman lafiya da magance kalubalen rashin tsaro da kuma samun ci gaba a kasa baki daya.

Daya daga cikin gwamnonin, gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya a nasa sakon Sallah ga al’ummar jiharsa, ya nanata bukatar ci gaba da yin addo’oin samun zaman zaman lafiya a jihar da kuma kasa baki daya.

  • Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
  • Sakon Sallah: Ina Aiki Dare Da Rana Don Ceto Nijeriya -Tinubu

Sakon nasa na kunshe ne cikin sanarwar da Darakta Janar na yada labaransa Ismaila Uba Misilli ya fitar.

Gwamnan wanda kuma shi ne shugaban kungiyar gwamnonin Arewacin Nijeriya, ya bukaci ‘yan uwa Musulmi da su taimaka wa gajiyayyu da marasa karfi, kamar Annabawan Allah SWA, Ibrahim AS da Muhammad S.A.W Allah ya kara masa aminci suka kwadaitar da Musulmi suma su yi.

Shi kuwa, gwamnan jihar Neja Mohammed Umaru Bago, ya yi kira ne ga Musulmi da su rungumi dabi’ar kauna yin da’a kamar yadda kakanmu Annabi Ibrahim AS ya kwatar da Musulmi.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

A nasa sakon, wanda sakatarensa na yada labarai Bologi Ibrahim ya fitar, gwamnan ya jaddada mahimmancin da babbar Sallar ta ke da shi, inda ya bukaci Musulmi da su yi amfani da damar don kara karfafa imaninsu da mika al’amuransu ga Allah SWA.

A nasa bangaren gwamnan jihar Filato, Barista Caleb Mutfwang ya yi kira ga Musulmi da su ci gaba da sadaukar da kawunansu wajen nuna kuna da son juna.

Mutfwang, a cikin sakon wanda Daraktansa na yada labarai Gyang Bere, ya fitar, ya bai wa ‘yan jihar tabbacin cewa, gwamnatinsa za ta ja kowa a jiki.

Shi ma gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq, ya taya Musulmi murnar bikin Sallah babba, inda ya ce Sallar na nuna yin imani ne da kuma mika wuya ga Allah SWA.

Shi kuwa gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello, ya bukaci ‘yan jihar da su rungumi dabi’ar yin kyauta ga marasa karfi da kuma sadaukar da kai.

Bello, a sakon nasa ya shawarci Musulmi da su rungumi koyarwar Annabi Muhammad SAW ya koyar.

Shi ma sakararen gwamnatin tarayya Sanata George Akume a cikin sanarwar da ya fitar, ya taya Musulmi muranar Sallah, inda ya bukace su da su yi amfani da lokutan Sallar wajen nuna kauna da sadaukar da kai don samun zaman lafiya a Nijeriya.

Ita kuwa kungiyar dattawan Arewa (ACF) ta ya Musulmi murnar babbar Sallah.

ACF a cikin sanarwar da shugabanta, Architect Gabriel Aduku ya fitar ya bukaci Musulmi da su rungumi dabi’ar samun zaman lafiya da kuma yi addu’oi don Allah ya kawo dauki ga tattain arzikin Nijeriya.

Shi ma shugaban hukumar jin dadin alhazai ta kasa (NAHCON), Alhaji Zikrullah Kunle Hassan a sakonsa ya ta ya daukacin Musulmin duniya murnar bikin babbar Sallah.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Sakon Sallah: Gwamnatinmu Za Ta Yi Wa Kowa Adalci -Mataimakin Gwamnan Kano

Sakon Sallah: Gwamnatinmu Za Ta Yi Wa Kowa Adalci -Mataimakin Gwamnan Kano

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version