• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnoni Sun Ta Ya Musulmin Nijeriya Murnar Sallah Babba

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnoni Sun Ta Ya Musulmin Nijeriya Murnar Sallah Babba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu daga cikin gwamnonin kasar nan, sun bukaci daukacin Musulmi da su yi amfani da lokutan Sallah wajen yin addu’oin samun zaman lafiya da magance kalubalen rashin tsaro da kuma samun ci gaba a kasa baki daya.

Daya daga cikin gwamnonin, gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya a nasa sakon Sallah ga al’ummar jiharsa, ya nanata bukatar ci gaba da yin addo’oin samun zaman zaman lafiya a jihar da kuma kasa baki daya.

  • Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
  • Sakon Sallah: Ina Aiki Dare Da Rana Don Ceto Nijeriya -Tinubu

Sakon nasa na kunshe ne cikin sanarwar da Darakta Janar na yada labaransa Ismaila Uba Misilli ya fitar.

Gwamnan wanda kuma shi ne shugaban kungiyar gwamnonin Arewacin Nijeriya, ya bukaci ‘yan uwa Musulmi da su taimaka wa gajiyayyu da marasa karfi, kamar Annabawan Allah SWA, Ibrahim AS da Muhammad S.A.W Allah ya kara masa aminci suka kwadaitar da Musulmi suma su yi.

Shi kuwa, gwamnan jihar Neja Mohammed Umaru Bago, ya yi kira ne ga Musulmi da su rungumi dabi’ar kauna yin da’a kamar yadda kakanmu Annabi Ibrahim AS ya kwatar da Musulmi.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

A nasa sakon, wanda sakatarensa na yada labarai Bologi Ibrahim ya fitar, gwamnan ya jaddada mahimmancin da babbar Sallar ta ke da shi, inda ya bukaci Musulmi da su yi amfani da damar don kara karfafa imaninsu da mika al’amuransu ga Allah SWA.

A nasa bangaren gwamnan jihar Filato, Barista Caleb Mutfwang ya yi kira ga Musulmi da su ci gaba da sadaukar da kawunansu wajen nuna kuna da son juna.

Mutfwang, a cikin sakon wanda Daraktansa na yada labarai Gyang Bere, ya fitar, ya bai wa ‘yan jihar tabbacin cewa, gwamnatinsa za ta ja kowa a jiki.

Shi ma gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq, ya taya Musulmi murnar bikin Sallah babba, inda ya ce Sallar na nuna yin imani ne da kuma mika wuya ga Allah SWA.

Shi kuwa gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello, ya bukaci ‘yan jihar da su rungumi dabi’ar yin kyauta ga marasa karfi da kuma sadaukar da kai.

Bello, a sakon nasa ya shawarci Musulmi da su rungumi koyarwar Annabi Muhammad SAW ya koyar.

Shi ma sakararen gwamnatin tarayya Sanata George Akume a cikin sanarwar da ya fitar, ya taya Musulmi muranar Sallah, inda ya bukace su da su yi amfani da lokutan Sallar wajen nuna kauna da sadaukar da kai don samun zaman lafiya a Nijeriya.

Ita kuwa kungiyar dattawan Arewa (ACF) ta ya Musulmi murnar babbar Sallah.

ACF a cikin sanarwar da shugabanta, Architect Gabriel Aduku ya fitar ya bukaci Musulmi da su rungumi dabi’ar samun zaman lafiya da kuma yi addu’oi don Allah ya kawo dauki ga tattain arzikin Nijeriya.

Shi ma shugaban hukumar jin dadin alhazai ta kasa (NAHCON), Alhaji Zikrullah Kunle Hassan a sakonsa ya ta ya daukacin Musulmin duniya murnar bikin babbar Sallah.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bikin Sallah BabbaGwamnoni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

Next Post

Sakon Sallah: Gwamnatinmu Za Ta Yi Wa Kowa Adalci -Mataimakin Gwamnan Kano

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

4 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

4 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

5 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

5 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

8 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

9 hours ago
Next Post
Sakon Sallah: Gwamnatinmu Za Ta Yi Wa Kowa Adalci -Mataimakin Gwamnan Kano

Sakon Sallah: Gwamnatinmu Za Ta Yi Wa Kowa Adalci -Mataimakin Gwamnan Kano

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.