ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnoni Sun Ta Ya Musulmin Nijeriya Murnar Sallah Babba

by Abubakar Abba
3 years ago
Sallah

Wasu daga cikin gwamnonin kasar nan, sun bukaci daukacin Musulmi da su yi amfani da lokutan Sallah wajen yin addu’oin samun zaman lafiya da magance kalubalen rashin tsaro da kuma samun ci gaba a kasa baki daya.

Daya daga cikin gwamnonin, gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya a nasa sakon Sallah ga al’ummar jiharsa, ya nanata bukatar ci gaba da yin addo’oin samun zaman zaman lafiya a jihar da kuma kasa baki daya.

  • Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
  • Sakon Sallah: Ina Aiki Dare Da Rana Don Ceto Nijeriya -Tinubu

Sakon nasa na kunshe ne cikin sanarwar da Darakta Janar na yada labaransa Ismaila Uba Misilli ya fitar.

ADVERTISEMENT

Gwamnan wanda kuma shi ne shugaban kungiyar gwamnonin Arewacin Nijeriya, ya bukaci ‘yan uwa Musulmi da su taimaka wa gajiyayyu da marasa karfi, kamar Annabawan Allah SWA, Ibrahim AS da Muhammad S.A.W Allah ya kara masa aminci suka kwadaitar da Musulmi suma su yi.

Shi kuwa, gwamnan jihar Neja Mohammed Umaru Bago, ya yi kira ne ga Musulmi da su rungumi dabi’ar kauna yin da’a kamar yadda kakanmu Annabi Ibrahim AS ya kwatar da Musulmi.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

A nasa sakon, wanda sakatarensa na yada labarai Bologi Ibrahim ya fitar, gwamnan ya jaddada mahimmancin da babbar Sallar ta ke da shi, inda ya bukaci Musulmi da su yi amfani da damar don kara karfafa imaninsu da mika al’amuransu ga Allah SWA.

A nasa bangaren gwamnan jihar Filato, Barista Caleb Mutfwang ya yi kira ga Musulmi da su ci gaba da sadaukar da kawunansu wajen nuna kuna da son juna.

Mutfwang, a cikin sakon wanda Daraktansa na yada labarai Gyang Bere, ya fitar, ya bai wa ‘yan jihar tabbacin cewa, gwamnatinsa za ta ja kowa a jiki.

Shi ma gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq, ya taya Musulmi murnar bikin Sallah babba, inda ya ce Sallar na nuna yin imani ne da kuma mika wuya ga Allah SWA.

Shi kuwa gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello, ya bukaci ‘yan jihar da su rungumi dabi’ar yin kyauta ga marasa karfi da kuma sadaukar da kai.

Bello, a sakon nasa ya shawarci Musulmi da su rungumi koyarwar Annabi Muhammad SAW ya koyar.

Shi ma sakararen gwamnatin tarayya Sanata George Akume a cikin sanarwar da ya fitar, ya taya Musulmi muranar Sallah, inda ya bukace su da su yi amfani da lokutan Sallar wajen nuna kauna da sadaukar da kai don samun zaman lafiya a Nijeriya.

Ita kuwa kungiyar dattawan Arewa (ACF) ta ya Musulmi murnar babbar Sallah.

ACF a cikin sanarwar da shugabanta, Architect Gabriel Aduku ya fitar ya bukaci Musulmi da su rungumi dabi’ar samun zaman lafiya da kuma yi addu’oi don Allah ya kawo dauki ga tattain arzikin Nijeriya.

Shi ma shugaban hukumar jin dadin alhazai ta kasa (NAHCON), Alhaji Zikrullah Kunle Hassan a sakonsa ya ta ya daukacin Musulmin duniya murnar bikin babbar Sallah.

Sallah
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Next Post
Sakon Sallah: Gwamnatinmu Za Ta Yi Wa Kowa Adalci -Mataimakin Gwamnan Kano

Sakon Sallah: Gwamnatinmu Za Ta Yi Wa Kowa Adalci -Mataimakin Gwamnan Kano

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.