ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnoni Sun Ta Ya Musulmin Nijeriya Murnar Sallah Babba

by Abubakar Abba
3 years ago
Sallah

Wasu daga cikin gwamnonin kasar nan, sun bukaci daukacin Musulmi da su yi amfani da lokutan Sallah wajen yin addu’oin samun zaman lafiya da magance kalubalen rashin tsaro da kuma samun ci gaba a kasa baki daya.

Daya daga cikin gwamnonin, gwamnan jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya a nasa sakon Sallah ga al’ummar jiharsa, ya nanata bukatar ci gaba da yin addo’oin samun zaman zaman lafiya a jihar da kuma kasa baki daya.

  • Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
  • Sakon Sallah: Ina Aiki Dare Da Rana Don Ceto Nijeriya -Tinubu

Sakon nasa na kunshe ne cikin sanarwar da Darakta Janar na yada labaransa Ismaila Uba Misilli ya fitar.

ADVERTISEMENT

Gwamnan wanda kuma shi ne shugaban kungiyar gwamnonin Arewacin Nijeriya, ya bukaci ‘yan uwa Musulmi da su taimaka wa gajiyayyu da marasa karfi, kamar Annabawan Allah SWA, Ibrahim AS da Muhammad S.A.W Allah ya kara masa aminci suka kwadaitar da Musulmi suma su yi.

Shi kuwa, gwamnan jihar Neja Mohammed Umaru Bago, ya yi kira ne ga Musulmi da su rungumi dabi’ar kauna yin da’a kamar yadda kakanmu Annabi Ibrahim AS ya kwatar da Musulmi.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

A nasa sakon, wanda sakatarensa na yada labarai Bologi Ibrahim ya fitar, gwamnan ya jaddada mahimmancin da babbar Sallar ta ke da shi, inda ya bukaci Musulmi da su yi amfani da damar don kara karfafa imaninsu da mika al’amuransu ga Allah SWA.

A nasa bangaren gwamnan jihar Filato, Barista Caleb Mutfwang ya yi kira ga Musulmi da su ci gaba da sadaukar da kawunansu wajen nuna kuna da son juna.

Mutfwang, a cikin sakon wanda Daraktansa na yada labarai Gyang Bere, ya fitar, ya bai wa ‘yan jihar tabbacin cewa, gwamnatinsa za ta ja kowa a jiki.

Shi ma gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq, ya taya Musulmi murnar bikin Sallah babba, inda ya ce Sallar na nuna yin imani ne da kuma mika wuya ga Allah SWA.

Shi kuwa gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello, ya bukaci ‘yan jihar da su rungumi dabi’ar yin kyauta ga marasa karfi da kuma sadaukar da kai.

Bello, a sakon nasa ya shawarci Musulmi da su rungumi koyarwar Annabi Muhammad SAW ya koyar.

Shi ma sakararen gwamnatin tarayya Sanata George Akume a cikin sanarwar da ya fitar, ya taya Musulmi muranar Sallah, inda ya bukace su da su yi amfani da lokutan Sallar wajen nuna kauna da sadaukar da kai don samun zaman lafiya a Nijeriya.

Ita kuwa kungiyar dattawan Arewa (ACF) ta ya Musulmi murnar babbar Sallah.

ACF a cikin sanarwar da shugabanta, Architect Gabriel Aduku ya fitar ya bukaci Musulmi da su rungumi dabi’ar samun zaman lafiya da kuma yi addu’oi don Allah ya kawo dauki ga tattain arzikin Nijeriya.

Shi ma shugaban hukumar jin dadin alhazai ta kasa (NAHCON), Alhaji Zikrullah Kunle Hassan a sakonsa ya ta ya daukacin Musulmin duniya murnar bikin babbar Sallah.

Sallah
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Sakon Sallah: Gwamnatinmu Za Ta Yi Wa Kowa Adalci -Mataimakin Gwamnan Kano

Sakon Sallah: Gwamnatinmu Za Ta Yi Wa Kowa Adalci -Mataimakin Gwamnan Kano

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.