• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Shawo Kan Matsalar Wutar Lantarki

by Shehu Yahaya
9 months ago
in Labarai
0
Gwamnonin Arewa Sun Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Shawo Kan Matsalar Wutar Lantarki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da jihohin Arewacin kasar nan suke ci gaba da fuskantar matsalar rashin wutar lantarki, wadda ta shafi ma’aikatun gwamnati da masana’antu da kuma harkokin kasuwancin al’ummar yankin arewa, da aka kwashe kwanaki babu hasken wutar lantarki a yankin, wasu na ganin shiryayyen lamari ne na yi wa tattalin arzikin yankin zagon kasa.

Kungiyar dattawan arewa (NEF) ta bayyana cewa matsalar rashin wutar lantarki a arewa shiryayyen lamari ne, inda suka ce an yi haka ne domin yi wa tattalin arzikin arewa zagon kasa.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Horor Da Kasar Sin Take Tallafawa Ya Inganta Yaki Da Nakiyoyin Da Aka Binne A Somaliya

A zantawarsa da wakilinmu, mai magana da yawun kungiyar dattawan Arewa, Abdul-Azeez Suleiman, ya ce, “Ga dukkan mai hankali da kuma kishin Arewa ya san zagon kasa ne da nufin gurgunta yankin. Idan aka yi la’akari da abubuwan da ke faruwa kafin rashin wutar, za a ga cewa rashin zaman lafiya ya hana noma, ya hana kiwo, ya hana karatu a Arewa. Yanzu ga wannan bakin duhu da aka jefa yankin a ciki.

“Masana sun tabbatar da cewa idan ana nufin gurgunta kasa ko yanki ko al’umma, matakin farko shi ne jefa ta cikin duhu. A yanzu a Arewa ba masana’antar da ke motsawa, ko nikan tuwo da garin kunu ya zama tashin hankali. Kun ga kenan duk matakai na gurgunta tattalin arziki da walwala da zaman lafiya duk sun bayyana. Sai dai fa Arewa ba ta da ikon zargin wani yanki game da wannan lamari.

Ya ci gaba da cewa, tun bayan mulkin su Sardauna Ahmadu Bello aka sami wadanda ba su damu da al’umma ba, sai kawunansu da iyalansu, suke ta sace dukiyoyi suna mayar da Arewa baya. Ya ce shugabannin Arewa su suka kashe duk ababen more rayuwa da Sardauna ya samar.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

Sai dai a nata bangaren, kungiyar gwamnonin Arewa ta nemi gwamnatin tarayya ta yi gaggawar shawo kan matsalar wutar lantarki da ake fama da ita a mafi yawan yankin.

Kungiyar ta yi kiran ne yayin taron da ta gudanar a fadar gwamnatin Jihar Kaduna karkashin jagorancin Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya.

Gwamnonin tare da sarakunan gargajiya na shiyyar Arewacin kasar nan sun tattauna matsalolin da suka dabaibaye yankin. Sama da kwana takwas kenan da jefa yankunan Arewa maso yamma, da Arewa maso gabas, da wani bangare na Arewa ta tsakiyar cikin duhu sakamakon lalacewar babban tashar samar da wutar lantarki ta kasa.

Gwamna Inuwa ya kara da cewa, “Kungiyar na kira ga gwamnatin tarayya da hukumomin da suka dace da su gaggauta shawo kan matsalar lantarki da mafi yawan jihohin arewaci ke ciki.

“Wannan lamari ba wai yana nuna girman hadarin rashin ababen more rayuwa ba ne kawai, yana kuma fito da bukatun gina wasu hanyoyin fadada samun wutar lantarki.”

A wata sanarwar da hukumar kula da wutar lantarki na Nijeriya (TCN) ta fitar, ta ce matsalar rashin wuta da ke addabar yankin Arewa za ta ci gaba saboda kalubalen tsaro da ke hana gyaran wasu muhimman layukan wutar.

Ya zuwa yanzu a Jihar Kaduna matsalar rashin wutar lantarki tana ci gaba da jefa al’umma cikin mawuyacin hali a yayin da harkokin kasuwanci suka yi tsaye cak.

Sai dai kuma matsalar ta kara yawaitar ‘yan ta’adda musamman masu kwacen wayar hannu a wuraren da ake yin cajin wayoyi.

Masu shagunan cajin waya sun shaida wa wakilinmu cewa a kullum suna zama cikin fargabar matasa masu zuwa da makamai suna kwace wayoyin mutane da suka kawo caji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaGwamnonin ArewaWutar Lantarki
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Gwamnati Da Kafafen Yaɗa Labarai Abokan Hulɗa Ne Ba Na Adawa Ba – Minista

Related

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
Labarai

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

6 minutes ago
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

1 hour ago
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

2 hours ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

3 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

18 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

21 hours ago
Next Post
Gwamnati Da Kafafen Yaɗa Labarai Abokan Hulɗa Ne Ba Na Adawa Ba – Minista

Gwamnati Da Kafafen Yaɗa Labarai Abokan Hulɗa Ne Ba Na Adawa Ba - Minista

LABARAI MASU NASABA

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

August 3, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

August 3, 2025
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

August 3, 2025
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

August 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

August 3, 2025
Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.