• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Nuna Ƙwarin Gwiwarsu Na Samar Da Kyakkyawar Makomar Yankin

by Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnonin Arewa sun bayyana kwarin gwiwarsu na cewa tare da goyon baya da hadin kai za su shawo kan duk wani kalubale kuma za su cimma burinsu na samar da makoma mai kyau ga yankin Arewa da Nijeriya baki daya.

Shugaban kungiyar kuma gwamnan jihar Gombe, Alhaji Mohammadu Inuwa Yahaya ne ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da jawabinsa a taron kungiyar da ya gudana a ranar Talata a gidan gwamnati a Kaduna.

  • NNPCL Ya Bayyana Ranar Da Matatar Man Fetur Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki
  • Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Sake Kutsawa Garin Abuja, Sun Sace Mutane 4

Alhaji Yahaya ya ce, gina dan Adam na da matukar muhimmanci ga ci gaban yankin, inda ya koka da cewa, a halin yanzu, Arewacin Nijeriya ne ke da mafi yawancin yaran da ba sa zuwa makaranta a duniya.

Gwamnan ya bayyana hakan da dewa, sam bai dace ba kuma dole ne a yi gaggawar magance wannan matsala, wanda ya ce, kowane yaro ya cancanci samun ingantaccen ilimi da kuma damar bunkasa fasahar da ake bukata don samun nasara.

Ya kara da cewa, bangaren tsaro yana kan gaba a abubuwan da kungiyar ta fifita, yana mai jaddada cewa, a taron da suka yi na karshe, kungiyar ta jaddada aniyarta na yin aiki tare da gwamnatin tarayya, domin samar da mafita mai dorewa kan kalubalen tsaro dake addabar yankin.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

A nasa jawabin, gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani ya bayyana cewa, taron ya ba su damar duba nasarori da kalubalen da suka samu kawo yanzu a yakin da ake da ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane da kuma kirkiro sabbin dabarun tunkarar wadannan makiya masu hana ci gaba.

Gwamna Sani ya sake nanata kiransa na tun farko ga kungiyar da su samar da dabaru da tsare-tsare na bai daya don magance matsalar rashin tsaro ta hanyar kafa Cibiyar Gudanarwa don daidaita ayyukan kungiyar na hadin gwiwa.

Ya bukaci takwarorinsa da su sake bullo da dabara domin cimma matsaya kan samar da tsarin bai daya na ci gaban Arewacin Nijeriya.

Daga cikin mahalarta taron, akwai Gwamnonin Bauchi, Zamfara, Katsina, Kaduna, Nasarawa, Gombe, Maiduguri yayin da Jigawa, Kano, Filato, yobe, Benuwe, Kwara, Neja, Adamawa da Sokoto, suka turo mataimakansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnonin ArewaTa'addancin 'yan bindigaTabarbarewar tsaro a ArewaYankin arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Serbia: Zan Rubuta Wani Littafi Don Tunawa Da Hulda Ta Da Xi Jinping

Next Post

Karancin Mai: Majalisa Ta Gayyaci Ministan Man Fetur

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

3 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

20 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Karancin Mai: Majalisa Ta Gayyaci Ministan Man Fetur

Karancin Mai: Majalisa Ta Gayyaci Ministan Man Fetur

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.