ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Nuna Ƙwarin Gwiwarsu Na Samar Da Kyakkyawar Makomar Yankin

by Sulaiman
2 years ago
Arewa

Gwamnonin Arewa sun bayyana kwarin gwiwarsu na cewa tare da goyon baya da hadin kai za su shawo kan duk wani kalubale kuma za su cimma burinsu na samar da makoma mai kyau ga yankin Arewa da Nijeriya baki daya.

Shugaban kungiyar kuma gwamnan jihar Gombe, Alhaji Mohammadu Inuwa Yahaya ne ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da jawabinsa a taron kungiyar da ya gudana a ranar Talata a gidan gwamnati a Kaduna.

  • NNPCL Ya Bayyana Ranar Da Matatar Man Fetur Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki
  • Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Sake Kutsawa Garin Abuja, Sun Sace Mutane 4

Alhaji Yahaya ya ce, gina dan Adam na da matukar muhimmanci ga ci gaban yankin, inda ya koka da cewa, a halin yanzu, Arewacin Nijeriya ne ke da mafi yawancin yaran da ba sa zuwa makaranta a duniya.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya bayyana hakan da dewa, sam bai dace ba kuma dole ne a yi gaggawar magance wannan matsala, wanda ya ce, kowane yaro ya cancanci samun ingantaccen ilimi da kuma damar bunkasa fasahar da ake bukata don samun nasara.

Ya kara da cewa, bangaren tsaro yana kan gaba a abubuwan da kungiyar ta fifita, yana mai jaddada cewa, a taron da suka yi na karshe, kungiyar ta jaddada aniyarta na yin aiki tare da gwamnatin tarayya, domin samar da mafita mai dorewa kan kalubalen tsaro dake addabar yankin.

LABARAI MASU NASABA

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

A nasa jawabin, gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani ya bayyana cewa, taron ya ba su damar duba nasarori da kalubalen da suka samu kawo yanzu a yakin da ake da ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane da kuma kirkiro sabbin dabarun tunkarar wadannan makiya masu hana ci gaba.

Gwamna Sani ya sake nanata kiransa na tun farko ga kungiyar da su samar da dabaru da tsare-tsare na bai daya don magance matsalar rashin tsaro ta hanyar kafa Cibiyar Gudanarwa don daidaita ayyukan kungiyar na hadin gwiwa.

Ya bukaci takwarorinsa da su sake bullo da dabara domin cimma matsaya kan samar da tsarin bai daya na ci gaban Arewacin Nijeriya.

Daga cikin mahalarta taron, akwai Gwamnonin Bauchi, Zamfara, Katsina, Kaduna, Nasarawa, Gombe, Maiduguri yayin da Jigawa, Kano, Filato, yobe, Benuwe, Kwara, Neja, Adamawa da Sokoto, suka turo mataimakansu.

Arewa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”
  • Sulaiman
    Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

MASU ALAKA

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
Manyan Labarai

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Next Post
Karancin Mai: Majalisa Ta Gayyaci Ministan Man Fetur

Karancin Mai: Majalisa Ta Gayyaci Ministan Man Fetur

LABARAI MASU NASABA

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.