ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Arewa Sun Nuna Ƙwarin Gwiwarsu Na Samar Da Kyakkyawar Makomar Yankin

by Sulaiman
2 years ago
Arewa

Gwamnonin Arewa sun bayyana kwarin gwiwarsu na cewa tare da goyon baya da hadin kai za su shawo kan duk wani kalubale kuma za su cimma burinsu na samar da makoma mai kyau ga yankin Arewa da Nijeriya baki daya.

Shugaban kungiyar kuma gwamnan jihar Gombe, Alhaji Mohammadu Inuwa Yahaya ne ya bayyana haka a lokacin da yake gabatar da jawabinsa a taron kungiyar da ya gudana a ranar Talata a gidan gwamnati a Kaduna.

  • NNPCL Ya Bayyana Ranar Da Matatar Man Fetur Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki
  • Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Sake Kutsawa Garin Abuja, Sun Sace Mutane 4

Alhaji Yahaya ya ce, gina dan Adam na da matukar muhimmanci ga ci gaban yankin, inda ya koka da cewa, a halin yanzu, Arewacin Nijeriya ne ke da mafi yawancin yaran da ba sa zuwa makaranta a duniya.

ADVERTISEMENT

Gwamnan ya bayyana hakan da dewa, sam bai dace ba kuma dole ne a yi gaggawar magance wannan matsala, wanda ya ce, kowane yaro ya cancanci samun ingantaccen ilimi da kuma damar bunkasa fasahar da ake bukata don samun nasara.

Ya kara da cewa, bangaren tsaro yana kan gaba a abubuwan da kungiyar ta fifita, yana mai jaddada cewa, a taron da suka yi na karshe, kungiyar ta jaddada aniyarta na yin aiki tare da gwamnatin tarayya, domin samar da mafita mai dorewa kan kalubalen tsaro dake addabar yankin.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

A nasa jawabin, gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani ya bayyana cewa, taron ya ba su damar duba nasarori da kalubalen da suka samu kawo yanzu a yakin da ake da ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane da kuma kirkiro sabbin dabarun tunkarar wadannan makiya masu hana ci gaba.

Gwamna Sani ya sake nanata kiransa na tun farko ga kungiyar da su samar da dabaru da tsare-tsare na bai daya don magance matsalar rashin tsaro ta hanyar kafa Cibiyar Gudanarwa don daidaita ayyukan kungiyar na hadin gwiwa.

Ya bukaci takwarorinsa da su sake bullo da dabara domin cimma matsaya kan samar da tsarin bai daya na ci gaban Arewacin Nijeriya.

Daga cikin mahalarta taron, akwai Gwamnonin Bauchi, Zamfara, Katsina, Kaduna, Nasarawa, Gombe, Maiduguri yayin da Jigawa, Kano, Filato, yobe, Benuwe, Kwara, Neja, Adamawa da Sokoto, suka turo mataimakansu.

Arewa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Karancin Mai: Majalisa Ta Gayyaci Ministan Man Fetur

Karancin Mai: Majalisa Ta Gayyaci Ministan Man Fetur

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.