• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin Da Ba Za Su Iya Biyan Mafi Ƙarancin Albashin Naira 70,000 A Nijeriya

by Sadiq
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnonin Da Ba Za Su Iya Biyan Mafi Ƙarancin Albashin Naira 70,000 A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da Shugaba Bola Tinubu ya gabatar da sabon mafi karancin albashi na Naira 70,000, wasu gwamnonin jihohin Nijeriya, sun bayyana cewa ba za su iya biyan wannan sabon albashin ba saboda matsalolin kudi. 

Ga jerin gwamnonin:

  • Lokuta Da Yawa Nakan Dakata In Yi Kuka Ma’ishi Kafin Na Ci Gaba Da Rubutu – Fatima Gurin
  • Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu

Jihar Gombe: Gwamna Inuwa Yahaya

Gwamna Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, ya ce gwamnatinsa ba za ta iya biyan sabon albashin Naira 70,000 ba saboda kudaden da jihar ke samu daga gwamnatin tarayya ba za su isa ba.

Yahaya, wanda kuma shi ne shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, ya ce biyan tsohon mafi karancin albashi na Naira 30,000 yana yi musu wahala.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Ya bayyana cewa da yawa daga cikin jihohi ba za su iya biyan karin albashin ba, duk da karin kudaden da suka samu daga gwamnatin tarayya a kwanan nan.

Jihar Nasarawa: Gwamna Abdullahi Sule

Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa, ya yanke shawarar jinkirta aiwatar da sabon tsarin mafi albashi na Naira 70,000 har zuwa shekarar 2026.

A baya, ya yi alkawarin fara biyan sabon albashin a wannan watan, tare da biyan bashin watannin da suka wuce.

Duk da haka, ya bayyana cewa jihar na bukatar kimanin Naira miliyan 200 domin biyan ma’aikata, wanda ya ce hakan ba zai yiwuwa jihar ta fara biyan sabon albashin a yanzu ba

Jihar Kogi: Gwamna Ahmed Usman Ododo

Gwamna Ahmed Usman Ododo na Jihar Kogi bai yanke shawara kan ko yaushe gwamnatinsa za ta fara biyan sabon mafi karancin Naira na 70,000 ba.

Kwamishinan kudi na jihar, Ashiwaju Ashiru Idris, ya ce ba a sanya ranar fara biyan sabon albashin ba.

Damuwar Masana’antu Masu Zaman Kansu

Kungiyar Masana’antu Masu Zaman Kansu (OPS), ita ma ta bayyana damuwa kan sabon albashin na Naira 70,000.

Sun ce zai yi wahala kamfanoni su iya biyan wannan sabon albashi ba tare da samun taimako na musamman ba.

Adewale-Smatt Oyerinde, mai magana da yawun Kungiyar Masu Daukar Ma’aikata ta Nijeriya (NECA), ya nuna damuwa kan yadda sabon tsari albashin zai jefa kamfanoni cikin matsalar kudi.

Martanin Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC)

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) a Jihar Legas, ta fayyace cewa mafi karancin albashin Naira 35,000 da ake biya a halin yanzu daban ne da sabon mafi karancin albashi na Naira 70,000 da mayar doka kwana nan.

Funmi Sessi, shugaban NLC na Jihar Legas, ya yi kira da a samar da tsarin albashin da ya dace da nau’ikan ayyuka da matakan albashi daban-daban.

Wannan yanayin ya bayyana matsalolin kudi da jihohi da masana’antu daban-daban ke fuskanta wajen kokarin gyara tsarin albashinsu zuwa sabon mafi karancin albashi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GwamnoniLabaraiMa'aikataMafi Karancin Albashi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Lokuta Da Yawa Nakan Dakata In Yi Kuka Ma’ishi Kafin Na Ci Gaba Da Rubutu – Fatima Gurin

Next Post

Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Sin Da Laos Da Myanmar Da Thailand Sun Gudanar Da Wani Taro

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

4 hours ago
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

5 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

7 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

9 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

11 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

12 hours ago
Next Post
Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Sin Da Laos Da Myanmar Da Thailand Sun Gudanar Da Wani Taro

Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Sin Da Laos Da Myanmar Da Thailand Sun Gudanar Da Wani Taro

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.