ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwarzuwar Shekarar 2025 Sanata Oluremi Tinubu

by Leadership Hausa
3 weeks ago
Tinubu

Adaidai lokacin da ake da ake fama da matsalar taɓarɓarewar tattalin arziƙi da rashin jin daɗin jama’a da kuma wahalhalun da suka biyo bayan sauye-sauyen da aka samu, Sanata Oluremi Tinubu ta kasance mai matuƙar tausayi da jin ƙai a tsarin harkokin mulki.  A matsayinta na Uwargidan Shugaban Nijeriya, ta nuna cewa; idan aka aiwatar da mulki ta hanyar kyakkyawan jagoranci da tausayi da kuma tarbiyya, zai iya taimakawa wajen samun walwala ga dukkannin al’ummar ƙasa.

Shirin nan na ‘Renewed Hope Initiatiɓe’, ya mayar da Ofishin Uwargidan Shugaban Ƙasar ya zama abin koyi wajen yin hidima ga ‘yan ƙasa mai matuƙar ma’ana. Aikin da take gudanarwar, ya ƙunshi taimaka wa waɗanda mazajensu suka mutu, suka bar su da ƙananan yara, ɗalibai, tsofaffi da kuma nakasassu a dukkanin faɗin Nijeriya.

Yadda Ake Gina Ɗan’adam

ADVERTISEMENT

Shirin ‘Renewed Hope Initiatiɓe’, ba aikin agaji ba ne; cibiyar sadar da jin kai ce ta ƙasa da aka ƙirƙira ta hanyar wani kyakkyawan tsari.  A 2025 kaɗai, ayyukanta sun haura na Naira  biliyan 25, wanda za a iya cewa; shi ne mafi girman aiki ko tallafin da uwargidan shugaban Nijeriya ta taɓa bayarwa.

Tun daga Jihar Kaduna zuwa Nasarawa, Benuwe zuwa Neja da kuma ma wasu jihohin, tawagar uwargidan shugaban ƙasar ta tallafa musu ta ɓangarori daban-daban.  Ko dai, bayar da ƙaramin jari ga ‘yan kasuwa, kayan agaji ga waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa ko kuma bayar da tallafin ilimi ga ɗalibai, wannan tsari nata ana aiwatar da shi cikin sauƙi kuma a tsare tare da bibiya.

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

  • Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Har ila yau, shirin nan nata Mata A Aikin Noma, ya bai wa matan karkara sama da 20,000 tallafi da horarwa da ƙara samun kuɗin shiga ga iyalai da kuma wadatar da al’umma. Kazalika, shirin Tallafin Ilimi, ya samar wa fiye da ɗalibai 3,000, guraben karatu, kwamfiyutoci da kuma jagoranci na gari. Ga tsofaffi kuma, Asusun Tallafa wa Tsofaffi ya bai wa tsofaffi 5,000 alawus-alawus da kula da lafiyarsu tare kuma da maido da martabar musamman waɗanda aka yi watsi da su, aka kuma manta da su.

Lokacin da iftila’i ya afku a Jihohin Filato da Benuwe a tsakiyar 2025, ba saƙo ta aike da shi; cikin gaggawa ta garzaya domin jajanta musu. Ta ziyarci waɗanda abin ya shafa, ta jajanta wa waɗanda suka rasa matsugunansu, sannan ta bayar da gudummawar Naira biliyan ɗaya ga kowace jihohin guda biyu. Daga baya a watan Agusta, ta ba da irin wannan agaji da ya kai kimanin Naira biliyan ɗaya ga al’ummomin da ambaliyar ruwa ta shafa a Jihar Neja tare da buhunhunan shinkafa da kayan sawa 2,000.

A watan Satumba, ta mayar da bikin cikarta shekaru 65 zuwa hidimar ƙasa, inda ta tara kuɗi kimanin  Naira biliyan 20.4, domin kammala ginin ɗakin karatu na ƙasa da aka daɗe ba a yi ba tare da yin watsi da shi a Abuja. Sannan, ta ƙi karɓar wasu kyaututtuka da aka ba ta, wanda hakan ke nuna kyakkyawan shugabanci na-gari.

Tausaya Wa Nakasassu

Tausayinta ga nakasassu ya bayyana a fili cikin shirin nan ‘Renewed Hope Initiatiɓe’, a ɓangaren nan na koyar da sana’a’i, wanda ya horar da aƙalla mutum 1,200 ilimin kwamfuta, samar da ‘yan kasuwa tare da horar da wasu.  Ta kuma ba da tallafin kiwon lafiya da wayar da kan jama’a tare da tantance ‘yan Nijeriya sama da 100,000 masu fama da cututtukan hawan jini, ciwon siga da kuma matsalar ido, domin tabbatar da ko suna ɗauke da cututtukan tare da ɗaukar matakan gaggawa.

Ta hanyar dagewa wajen ganin shirin ya tafi yadda ya kamata, Sanata Tinubu ta gabatar da kyakkyawan tsari, domin aiwatar da ayyukan jin ƙai.  Dagewarta kan nuna gaskiya, ya sa shirin RHI ya samu karramawa daga ƙungiyoyin farar hula da sauran abokan ci gaban ƙasa da ƙasa.

Sabunta Harkokin Ilimi

Tsohuwar malamar makaranta, Sanata Tinubu na kallon ajujuwa a matsayin wurin da aka samar da sabbin sauye-sauye.  Shirin da ta samar na matasa masu ilimi, wanda aka ƙaddamar a shekarar 2024, aka kuma sake faɗaɗa shi a 2025, na tallafa wa ɗalibai masu hazaƙa, waɗanda iyayensu ke da ƙaramin ƙarfi (Talakawa), wanda ya dace da su tare da ba su shawarwari, musamman ta fuskar harkar ilimin kimiyya da fasaha.  Fiye da ɗalibai 1,200 a halin yanzu sun samu damar shiga shirin, wanda ke nuni da cewa; sama da kashi 95 cikin 100 na waɗanda suka rabauta, ba su taɓa mantawa da wannan abin alhairi da aka yi musa ba.

Tasirin Abin Da Za A Iya Ƙirgawa Da Kuma Wanda Ke Shafar Ruwa Kai Tsaye

A duk fadin Najeriya, za a iya ƙirga ayyukanta, ba kawai a ƙididdiga ba, a cikin labarai.

Mata manoma 20,000 a halin yanzu, suna samun kuɗin shiga akai-akai, saboda tallafin noma da horo na RHI.  Dubban ɗalibai, sun faɗa kasadar ficewa daga makarantusu, amma yanzu ƙarƙashin wannan shiri nata, sun koma azuzuwansu sakamakon bayar da tallafin karatun da ta yi.   

Haka zalika, sama da ‘yan Nijeriya 100,000 ne aka yi wa gwajin kamuwa da cututtuka masu tsanani daban-daban, sannan da dama daga cikinsu sun samu tallafin ceton rai. Yanzu haka, tsofaffi dubu biyar ne ke cin gajiyar alawus-alawus na yau da kullun da kuma zuwa duba lafyarsu, yayin da nakasassu kuma aka ba su kayan aiki, domin fara sana’o’insu, wasu kuma da kansu sun zama masu horar da su.

A kowane irin hali, alƙalumman na ba da labari iri guda: a ƙarƙashin Sanata Tinubu, tausayi ya zama shi ne abin aunawa, sannan kuma abubuwan da ake sa rai da su, sun tabbata.

Imani, Iyali da kuma Amfanin Shugabanci

Kasancewarta mai tsananin tausayi da gaskiya, jagora tagari, mai kuma son yin aiki ta hanyar yin haɗin gwiwa, Sanata Tinubu na ɗaya daga cikin waɗanda ke jagorantar al’ummar da samar da haɗin kai tare da tausayinsu.  Ta auri Shugaba Bola Ahmed Tinubu, sannan ta daidaita buƙatun shugabancin ƙasa da iyali, imani da kuma tawali’u.

Nutsuwa da halinta da kuma ɗabi’un aikinta, sun haifar da sha’awa; har ma daga masu suka, suna sake fasalin ofishin Uwargidan Shugabancin a matsayin ɗaya daga cikin kulawa, maimakon alama.  Ta nuna cewa, mulki a cikin lumana, ka iya haifar da sakamako mai kyau tare da kuma tausayi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Next Post
Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano

Gobara Ta Tafka Ɓarna A Kasuwar Shuwaki, Ta Ƙona Fiye da Rumfuna 500 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.