ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

by Hussein Yero
7 months ago
Ɗakin

Uwargidan shugaban ƙasa, Sanata Remi Tinubu, ta ƙaddamar da ɗakin karatu na zamani na E-learning a Gusau, babban birnin Jihar Zamfara.

Uwargidan gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal ce, ta wakilci Sanata Remi Tinubu a wajen taron.

  • An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15
  • Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

Ta yaba da wannan shiri na ilimin zamani da Gwamnatin Tarayya ta kawo, inda ta ce zai taimaka wajen bunƙasa ci gaban ƙasa baki ɗaya.

ADVERTISEMENT

Hajiya Huriyya ta ce wannan ɗakin karatu na zamani na E-learning na daga cikin waɗanda aka kafa a jihohi 10 a ƙasar nan, ƙarƙashin shirin Renewed Hope Initiative tare da haɗin gwiwar Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA).

Ta bayyana cewa, shirin ba wai game da fasaha kawai ba ne, yana nufin ƙarfafa matasa da buɗe musu sabbin hanyoyin ilimi da ƙirƙire-ƙirƙire a Jihar Zamfara da ƙasar baki ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Ta ce, ta hanyar wannan E-library, ɗalibai, malamai da masu bincike za su samu damar amfani da bayanai da ilimin zamani cikin sauƙi.

A cewarta, Renewed Hope Initiative wanda Sanata Oluremi Tinubu ke jagoranta, na da manufar tallafa wa ilimi, ƙirƙire-ƙirƙire da ci gaban al’umma.

Wannan ɗakin karatu, in ji ta, alamar hangen nesan uwargidan shugaban ƙasa ne wajen inganta ilimi a Nijeriya.

Ta gode wa ma’aikatar sadarwa, ƙirƙire-ƙirƙire da tattalin arziƙin zamani, da kuma NITDA, saboda yadda suka aiwatar da aikin cikin nasara.

Ta kuma yaba wa mijinta, Gwamna Dauda Lawal, bisa jajircewarsa wajen kawo ci gaba a ɓangaren ilimi a Zamfara.

A nasa jawabin, Daraktan NITDA, Kashifu Inuwa, ya buƙaci ɗalibai da malamai a Zamfara da su yi amfani da wannan ɗakin karatu yadda ya kamata domin amfaninsu.

Shi ma Kwamishinan Ilimi na Kimiyya da Fasaha, Mallam Wadatau Madawaki, wanda Sakatariyar Dindindin Maryam Shantali ta wakilta, ya ce aikin ya yi daidai da manufofin Gwamna Dauda Lawal wanda tun zuwansa mulki ya bai wa ilimi fifiko.

Ta ƙara da cewa, a madadin ma’aikatar ilimi da al’ummar Zamfara, suna godiya ga Uwargidan shugaban ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, saboda kawo wannan shiri mai amfani.

Ta tabbatar da cewa ɗalibai, malamai, da masu bincike za su yi amfani da wannan ɗakin karatu yadda ya dace domin amfanin ilimi a jihar.

Ɗakin
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Jakadun Wayar Da Kai Game Da Rigakafi
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Ramadan: Hon Jaji Ya Ƙaddamar Da Tallafin Abinci Ga Mutane Sama Da 500,000 A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Dauda Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Almajirai 17 Da Suka Rasu A Sakamakon Tashin Gobara A Zamfara

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.