ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

by Hussein Yero
11 months ago
Ɗakin

Uwargidan shugaban ƙasa, Sanata Remi Tinubu, ta ƙaddamar da ɗakin karatu na zamani na E-learning a Gusau, babban birnin Jihar Zamfara.

Uwargidan gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal ce, ta wakilci Sanata Remi Tinubu a wajen taron.

  • An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15
  • Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

Ta yaba da wannan shiri na ilimin zamani da Gwamnatin Tarayya ta kawo, inda ta ce zai taimaka wajen bunƙasa ci gaban ƙasa baki ɗaya.

ADVERTISEMENT

Hajiya Huriyya ta ce wannan ɗakin karatu na zamani na E-learning na daga cikin waɗanda aka kafa a jihohi 10 a ƙasar nan, ƙarƙashin shirin Renewed Hope Initiative tare da haɗin gwiwar Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA).

Ta bayyana cewa, shirin ba wai game da fasaha kawai ba ne, yana nufin ƙarfafa matasa da buɗe musu sabbin hanyoyin ilimi da ƙirƙire-ƙirƙire a Jihar Zamfara da ƙasar baki ɗaya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ta ce, ta hanyar wannan E-library, ɗalibai, malamai da masu bincike za su samu damar amfani da bayanai da ilimin zamani cikin sauƙi.

A cewarta, Renewed Hope Initiative wanda Sanata Oluremi Tinubu ke jagoranta, na da manufar tallafa wa ilimi, ƙirƙire-ƙirƙire da ci gaban al’umma.

Wannan ɗakin karatu, in ji ta, alamar hangen nesan uwargidan shugaban ƙasa ne wajen inganta ilimi a Nijeriya.

Ta gode wa ma’aikatar sadarwa, ƙirƙire-ƙirƙire da tattalin arziƙin zamani, da kuma NITDA, saboda yadda suka aiwatar da aikin cikin nasara.

Ta kuma yaba wa mijinta, Gwamna Dauda Lawal, bisa jajircewarsa wajen kawo ci gaba a ɓangaren ilimi a Zamfara.

A nasa jawabin, Daraktan NITDA, Kashifu Inuwa, ya buƙaci ɗalibai da malamai a Zamfara da su yi amfani da wannan ɗakin karatu yadda ya kamata domin amfaninsu.

Shi ma Kwamishinan Ilimi na Kimiyya da Fasaha, Mallam Wadatau Madawaki, wanda Sakatariyar Dindindin Maryam Shantali ta wakilta, ya ce aikin ya yi daidai da manufofin Gwamna Dauda Lawal wanda tun zuwansa mulki ya bai wa ilimi fifiko.

Ta ƙara da cewa, a madadin ma’aikatar ilimi da al’ummar Zamfara, suna godiya ga Uwargidan shugaban ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, saboda kawo wannan shiri mai amfani.

Ta tabbatar da cewa ɗalibai, malamai, da masu bincike za su yi amfani da wannan ɗakin karatu yadda ya dace domin amfanin ilimi a jihar.

Ɗakin
Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Jakadun Wayar Da Kai Game Da Rigakafi
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Ramadan: Hon Jaji Ya Ƙaddamar Da Tallafin Abinci Ga Mutane Sama Da 500,000 A Zamfara
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero-2/
    Dauda Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Almajirai 17 Da Suka Rasu A Sakamakon Tashin Gobara A Zamfara

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.