• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, a kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya kai ziyara kasar Rasha, inda ya gana da takwaransa na kasar Vladimir Putin. Dangane da wannan batu, wane irin ra’ayi su kasashen yamma za su dauka, wannan ba sai na fada ba, ku ma za ku sani. Sai dai a nan za mu kyale ra’ayinsu, domin ina so in nuna muku wasu ra’ayoyi daga ‘yan Afirka.

An gudanar da wani taro mai taken “ Dimokuradiya: tunani mai daraja na daukacin dan Adam” a birnin Beijing na kasar Sin a kwanan nan, inda na samu damar tattauna da wasu masana da ‘yan siyasa na kasashen Afirka wadanda suka halarci taron, kuma na tambaye su kan ra’ayinsu dangane da ziyarar shugaba Xi a wannan karo. Sa’an nan Mista Charles Onunaiju, shehun malami mai nazarin harkoki masu alaka da kasar Sin na Najeriya, ya gaya mana cewa, hadin gwiwar kasashen Sin da Rasha ta sa ake samun daidaituwa a duniya, wadda ke taimakawa samar da wani yanayi na kwanciyar hankali. Ya ce idan babu hadin kan Sin da Rasha, za a samu karin juyin mulki, da tashin hankali, da rushewar tattalin arziki a wurare daban daban, sakamakon yadda wasu kasashen yamma suke cin kare babu babaka.

A nashi bangaren, shugaban jam’iyyar Socialist ta kasar Zambia, Dokta Fred M’membe, ya ce, shugabannin kasashen Sin da Rasha suna kokarin jagorantar aikin neman samun karin bangarori masu fada a ji a duniya. Ta yin la’akari da yadda dimbin kasashe irinsu India, da Brazil su ma suke shiga a dama da su, ana iya cewa, ba za a iya hana irin yanayi na samun karin bangarori masu tasiri a duniya ba.

Ban da haka, Kugiza Kaheru, mamban kwamitin kare hakkin dan Adam na kasar Uganda, ya gaya mana cewa, “Shugaba Xi Jinping yana neman ganin an daidaita rikicin da ake samu tsakanin Rasha da Ukraine ta hanyar sulhu. Wannan buri ne mai kyau, ya kamata a goyi bayansa, maimakon daukar matakai na soja.”

Wadannan mutane sun zo daga yammaci da gabashin Afirka, wadanda suka kasance masana ko kuma ‘yan siyasa. Sai dai dukkansu sun nuna goyon baya ga yadda ake yin hadin gwiwa tsakanin kasashen Sin da Rasha, da kokarin kasar Sin na neman tabbatar da zaman lafiya.

Labarai Masu Nasaba

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

Bayan mun tattauna ra’ayi na ‘yan Afirka, bari mu duba ainihin sakamakon da aka samu daga ziyarar shugaba Xi Jinping a kasar Rasha. Bisa labaran da aka watsa, da farko dai, ban da sanar da burin karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen Sin da Rasha, shugabannin 2 sun yi alkawarin aiwatar da ra’ayi na kasancewar bangarori masu fada a ji da yawa a duniya, da tabbatar da dimokuradiyya yayin da ake gudanar da harkokin kasa da kasa, ta yadda za a samar da karin gudunmowa ga aikin neman ci gaban al’ummar dan Adam.

Na biyu, shi ne shugabannin 2 sun sa hannu kan wata hadaddiyar sanarwa, inda suka jaddada bukatar daidaita rikicin kasar Ukraine ta hanyar yin shawarwari. A hakika, wadannan sakamakon da aka samu sun zama daya da hasashen da masana da ‘yan siyasa na kasashen Afirka suka yi.

Sa’an nan idan mun kwatanta ra’ayi na wasu ‘yan Afirka wanda muka ambata a baya, da hakikanin abun da ke faruwa, muna iya gano cewa, Afirka ta riga ta canza, inda kasashen yamma, tsoffin ‘yan mulkin mallaka, suka fara rasa damar yin tasiri kan tunanin mutanen kasashen Afirka. Yanzu masana da ‘yan siyasa na kasashen Afirka suna iya yin tunani kan harkokin kasa da kasa yadda ake bukata, don kare moriyar kasashen Afirka, da fahimtar gaskiyar abubuwa.

Ana samun sauyawar yanayi, ko da yake kafofin watsa labaru na kasashen Afirka na ci gaba da yin amfani da bayanan da takwarorinsu na kasashen yamma suka hada, kana ana samun cacar baki a kasashen Afirka, tsakanin masu goyon bayan kasashen yamma, da wadanda suke kin amincewa da su.

Dangane da sauyawar yanayin da ake samu, ina so in ambaci wani misali na daban: A kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da shawarar wayewar kai ta duniya, inda ya yi kira da a girmama yanayi na samun mabambantan wayewar kai a duniya, da amince da zabin kasa da kasa na neman wata dabara mai kima ta raya kansu. Wannan shawara ta samu goyon baya sosai daga masana, da ‘yan siyasa na kasashen Afirka, wadanda a wajen taron “ Dimokuradiya: tunani mai daraja na daukacin dan Adam”, suka tsaya kan cewar, babu wani daidaitaccen tsarin dimokuradiya daya tilo. Hakika ya kamata a lura da tarihi na wata kasa, da kokarin biyan bukatar kasar wajen daidaita matsalolinta, da lura da halayyar musamman ta wata kasa, da karfafa fahimtar juna, da hadin kai, tsakanin al’ummu daban daban, yayin da ake raya harkar dimokuradiya a wata kasa. Kar a ba wasu kasashen damar shawo kan sauran kasashe, ta fakewa da maganar dimokuradiya.

Yadda ake samun ra’ayi na bai daya tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, ya nuna cewa ra’ayi na mai da kasashen yamma cibiyar duniya ya zama tsohon yayi, yayin da karin kasashe masu tasowa ke neman tabbatar da tsarin dimokuradiya a duniya, da kasancewar mabambantan tunani game da al’adu da siyasa a kasashe daban daban, bisa bukatarsu ta raya kansu.

Gyare-gyare su kan faru ne bisa samun sauyawar tunanin mutum. Idan kun yarda da ni, wajen ganin rashin dimokuradiyya, da adalci, a harkokin kasa da kasa, to, sauyawar yanayin da ake samu yanzu shi ne ainihin abun da muke bukata. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

Next Post

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

Related

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya
Daga Birnin Sin

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

17 hours ago
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

19 hours ago
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
Daga Birnin Sin

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

21 hours ago
Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital

21 hours ago
“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki
Daga Birnin Sin

“Ruhin Sin Da Tsakiyar Asiya” Ya Jagoranci Bude Wani Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Yanki

22 hours ago
Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Sakamakon Ziyarar Shugaba Xi A Kazakhstan

23 hours ago
Next Post
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

June 19, 2025
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

June 19, 2025
Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

June 19, 2025
Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

June 19, 2025
Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

June 19, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

June 19, 2025
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi

June 18, 2025
WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

WTO Na Darajanta Tallafin Kasar Sin a Bangaren Cinikayya Ga Kasashe Masu Tasowa

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.