• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina, a kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya kai ziyara kasar Rasha, inda ya gana da takwaransa na kasar Vladimir Putin. Dangane da wannan batu, wane irin ra’ayi su kasashen yamma za su dauka, wannan ba sai na fada ba, ku ma za ku sani. Sai dai a nan za mu kyale ra’ayinsu, domin ina so in nuna muku wasu ra’ayoyi daga ‘yan Afirka.

An gudanar da wani taro mai taken “ Dimokuradiya: tunani mai daraja na daukacin dan Adam” a birnin Beijing na kasar Sin a kwanan nan, inda na samu damar tattauna da wasu masana da ‘yan siyasa na kasashen Afirka wadanda suka halarci taron, kuma na tambaye su kan ra’ayinsu dangane da ziyarar shugaba Xi a wannan karo. Sa’an nan Mista Charles Onunaiju, shehun malami mai nazarin harkoki masu alaka da kasar Sin na Najeriya, ya gaya mana cewa, hadin gwiwar kasashen Sin da Rasha ta sa ake samun daidaituwa a duniya, wadda ke taimakawa samar da wani yanayi na kwanciyar hankali. Ya ce idan babu hadin kan Sin da Rasha, za a samu karin juyin mulki, da tashin hankali, da rushewar tattalin arziki a wurare daban daban, sakamakon yadda wasu kasashen yamma suke cin kare babu babaka.

A nashi bangaren, shugaban jam’iyyar Socialist ta kasar Zambia, Dokta Fred M’membe, ya ce, shugabannin kasashen Sin da Rasha suna kokarin jagorantar aikin neman samun karin bangarori masu fada a ji a duniya. Ta yin la’akari da yadda dimbin kasashe irinsu India, da Brazil su ma suke shiga a dama da su, ana iya cewa, ba za a iya hana irin yanayi na samun karin bangarori masu tasiri a duniya ba.

Ban da haka, Kugiza Kaheru, mamban kwamitin kare hakkin dan Adam na kasar Uganda, ya gaya mana cewa, “Shugaba Xi Jinping yana neman ganin an daidaita rikicin da ake samu tsakanin Rasha da Ukraine ta hanyar sulhu. Wannan buri ne mai kyau, ya kamata a goyi bayansa, maimakon daukar matakai na soja.”

Wadannan mutane sun zo daga yammaci da gabashin Afirka, wadanda suka kasance masana ko kuma ‘yan siyasa. Sai dai dukkansu sun nuna goyon baya ga yadda ake yin hadin gwiwa tsakanin kasashen Sin da Rasha, da kokarin kasar Sin na neman tabbatar da zaman lafiya.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Bayan mun tattauna ra’ayi na ‘yan Afirka, bari mu duba ainihin sakamakon da aka samu daga ziyarar shugaba Xi Jinping a kasar Rasha. Bisa labaran da aka watsa, da farko dai, ban da sanar da burin karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen Sin da Rasha, shugabannin 2 sun yi alkawarin aiwatar da ra’ayi na kasancewar bangarori masu fada a ji da yawa a duniya, da tabbatar da dimokuradiyya yayin da ake gudanar da harkokin kasa da kasa, ta yadda za a samar da karin gudunmowa ga aikin neman ci gaban al’ummar dan Adam.

Na biyu, shi ne shugabannin 2 sun sa hannu kan wata hadaddiyar sanarwa, inda suka jaddada bukatar daidaita rikicin kasar Ukraine ta hanyar yin shawarwari. A hakika, wadannan sakamakon da aka samu sun zama daya da hasashen da masana da ‘yan siyasa na kasashen Afirka suka yi.

Sa’an nan idan mun kwatanta ra’ayi na wasu ‘yan Afirka wanda muka ambata a baya, da hakikanin abun da ke faruwa, muna iya gano cewa, Afirka ta riga ta canza, inda kasashen yamma, tsoffin ‘yan mulkin mallaka, suka fara rasa damar yin tasiri kan tunanin mutanen kasashen Afirka. Yanzu masana da ‘yan siyasa na kasashen Afirka suna iya yin tunani kan harkokin kasa da kasa yadda ake bukata, don kare moriyar kasashen Afirka, da fahimtar gaskiyar abubuwa.

Ana samun sauyawar yanayi, ko da yake kafofin watsa labaru na kasashen Afirka na ci gaba da yin amfani da bayanan da takwarorinsu na kasashen yamma suka hada, kana ana samun cacar baki a kasashen Afirka, tsakanin masu goyon bayan kasashen yamma, da wadanda suke kin amincewa da su.

Dangane da sauyawar yanayin da ake samu, ina so in ambaci wani misali na daban: A kwanan baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da shawarar wayewar kai ta duniya, inda ya yi kira da a girmama yanayi na samun mabambantan wayewar kai a duniya, da amince da zabin kasa da kasa na neman wata dabara mai kima ta raya kansu. Wannan shawara ta samu goyon baya sosai daga masana, da ‘yan siyasa na kasashen Afirka, wadanda a wajen taron “ Dimokuradiya: tunani mai daraja na daukacin dan Adam”, suka tsaya kan cewar, babu wani daidaitaccen tsarin dimokuradiya daya tilo. Hakika ya kamata a lura da tarihi na wata kasa, da kokarin biyan bukatar kasar wajen daidaita matsalolinta, da lura da halayyar musamman ta wata kasa, da karfafa fahimtar juna, da hadin kai, tsakanin al’ummu daban daban, yayin da ake raya harkar dimokuradiya a wata kasa. Kar a ba wasu kasashen damar shawo kan sauran kasashe, ta fakewa da maganar dimokuradiya.

Yadda ake samun ra’ayi na bai daya tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, ya nuna cewa ra’ayi na mai da kasashen yamma cibiyar duniya ya zama tsohon yayi, yayin da karin kasashe masu tasowa ke neman tabbatar da tsarin dimokuradiya a duniya, da kasancewar mabambantan tunani game da al’adu da siyasa a kasashe daban daban, bisa bukatarsu ta raya kansu.

Gyare-gyare su kan faru ne bisa samun sauyawar tunanin mutum. Idan kun yarda da ni, wajen ganin rashin dimokuradiyya, da adalci, a harkokin kasa da kasa, to, sauyawar yanayin da ake samu yanzu shi ne ainihin abun da muke bukata. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

Next Post

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

Related

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

11 hours ago
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

12 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

14 hours ago
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya
Daga Birnin Sin

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

15 hours ago
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
Daga Birnin Sin

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

16 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

17 hours ago
Next Post
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

LABARAI MASU NASABA

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

July 12, 2025
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.