• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
in Daga Birnin Sin
0
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da cewa ba a kammala cimma matsaya ba a tattaunawar kasar Sin da Amurka kan alakarsu ta kasuwanci da tattalin arziki, amma sakamakon da ake samu a baya-bayan nan alama ce mai karfafa gwiwa ga al’ummomin duniya masu neman ganin an rage fargabar rashin tabbas da ake kaka-ni-ka-yi a ciki a fagen kasa da kasa. Kara wa’adin jingine karin haraji daga sassan biyu na tsawon kwanaki 90, ya sake farfado da fatan samun kwanciyar hankali mai inganci a fannin tattalin arziki tsakanin manyan kasashen biyu.

Kasashe da dama, wadanda suka tsinci kansu a tsaka-mai-wuya sakamakon tataburzar kasuwancin Sin da Amurka, sun jima suna kira ga bangarorin biyu da su kara kaimi. Abin da ake tsammani a bayyane yake: gudanar da dangantakar tattalin arziki tsakanin kasashen biyu bisa sauke nauyin da ya rataya a wuyar ko wane bangare, da nuna gaskiya, da hangen nesa. Duniya ta zuba ido tana jiran ganin samun kyakkyawan sakamako a tattaunawar kasashen biyu.

Sin da Amurka a matsayinsu na manyan kasashe biyu masu karfin tattalin arziki a duniya, su ne ginshikan cinikayya, da zuba jari, da kirkire-kirkiren sabbin fasahohi. Dangantakar tattalin arzikin kasashen biyu ba kawai tana shafar muradun cikin gidansu ba ne kawai, kanwa ce uwar-gami ga tabbatar da zaman lafiyar duniya. Don haka ne kasashe da dama, tun daga masu tasowa zuwa sauran kasashe masu karfin tattalin arziki, suka sa ido sosai tare da yin kira ga kasashen biyu da su dawo da tafiyar da harkokin tattalin arzikinsu cikin tsanaki da hangen nesa.

Dambarwar kasuwancin kasashen biyu ta haifar da rudani ga tsarin samar da kayayyaki a duniya, da masana’antu tun daga kan na kimiyya da fasaha musamman a bangaren na’urorin kera kayan laturoni na semiconductors, da kere-keren fasahar AI har zuwa kayan noma da sauran na amfanin yau da kullum. Kazalika, an shiga rashin tabbas a bangaren kasuwannin hannayen jari na duniya, da canjin kudi, da kuma sauye-sauyen ra’ayoyin masu saka jari.

Kamar yadda kasar Sin ta sha nanatawa, babu wanda zai yi nasara a yakin cinikayya da kasuwanci, kuma ya dace Amurka ta rika sauke nauyin dake wuyanta. Rura wutar yake-yaken kasuwanci da kakaba takunkumai, ba su da wata ma’ana sai tayar da zaune tsaye, da sabbaba tsadar kayayyaki, da haifar da koma bayan tattalin arziki. Duk da cewa, Sin ta fito baro-baro a fili ta shaida cewa ba ta tsoron gwabzawa, amma tana ci gaba da yekuwar tabbatar da damawa da kasashe daban-daban a harkokin duniya. Kasashen duniya sun amince da tsarin ciniki na duniya wanda ya dogara da ka’idojin dake karkashin kulawar hukumar kasuwanci ta duniya (WTO). Idan ma akwai wasu sauye-sauye na manufofi musamman a kan kayayyakin da ake fitarwa daga kasashe, kamata ya yi a tattauna a tsakani domin samun maslaha amma ba yin gaban-kai kamar yadda Amurka ke nunawa saboda rashin mafadi ba.

Labarai Masu Nasaba

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Muryoyi daga ko’ina cikin duniya sun nemi a warware matsalar bisa turbar adalci. Shugabannin tarayyar Turai sun yi ta kira ga kasashen Sin da Amurka da su kiyaye bude kasuwanni da gudanar da gasa ta gaskiya. Kasashen kudu maso gabashin Asiya, sun ba da shawarar tabbatar da kwanciyar hankali. Kasashen Afirka da na Latin Amurka sun nuna damuwa da halin da ake ciki saboda barazanar da lamarin yake yi ga damarmakin zuba jari da kasuwancin kasashensu.

Gyaruwar dangantakar tattalin arziki tsakanin Sin da Amurka za ta iya haifar da wani sabon zamani na hadin gwiwa, da kirkire-kirkire, da ci gaban da ya kunshi kasashen duniya baki daya. A wannan duniyar tamu wadda bukatar hada hannu da juna ke kara bayyana, kiran a bayyane yake, wato duniya tana bukatar Sin da Amurka ba kawai don zama tare ba, har ma su zama ababen buga misali a bangaren aiki tare. (Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

Next Post

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu

Related

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo
Daga Birnin Sin

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

58 minutes ago
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta
Daga Birnin Sin

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

2 hours ago
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

3 hours ago
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

5 hours ago
Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan
Daga Birnin Sin

Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

6 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

1 day ago
Next Post
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Ta Bayyana Rashin Gamsuwa Da Manufar Shugaba Trump Ta Korar Marasa Galihu

LABARAI MASU NASABA

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.