• English
  • Business News
Saturday, May 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwa Ce Tsakanin Sin da Afirka Ba Mulkin Mallaka ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Hadin Gwiwa Ce Tsakanin Sin da Afirka Ba Mulkin Mallaka ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen ba da gudummawa ga ci gaban Afirka ta hanyar ginawa da gyara muhimman ababen more rayuwa kamar madatsun ruwa da tituna da asibitoci, wadanda suka karfafa dunkulewar yankin, da habaka cinikayya da masana’antu. Don haka, yawancin kasashen Afirka suna daraja hadin gwiwarsu da kasar Sin, saboda tana goyon bayan manufofinsu na ci gaba. A fannin kiwon lafiya, tallafin jinya na kasar Sin ya inganta samun damammaki da walwala ga yawancin kasashen Afirka. Haka ma, shirye-shiryen horar da ilimi da fasaha, irin su tallafin karatu da kafa cibiyoyin Confucius da na Luban da dai sauransu sun inganta jarin dan Adam tare da tallafawa ayyukan zamanantar da Afirka.

 

Hadin gwiwar Sin da Afirka ta haifar da nasarori mara misaltuwa wandanda suka rusa ikirarin kafafen yada labaran kasashen yammacin duniya na cewa kasar Sin tana “mallakar” Afirka. Hasali ma, hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka ya zama misalin dangantakar dake tsakanin kasa da kasa bisa daidaito ba tare da mamaya ba, wadda ke nuna sabon salo na sahihin tsarin hadin gwiwar dake tsakanin kasashen duniya, wadda kuma ta ginu bisa mutunta juna da samun moriyar juna. A gun taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka ko FOCAC na shekarar 2024 da za a gudanar daga ranar 4 zuwa ta 6 ga wannan wata, shugabannin bangarorin biyu za su yi musayar ra’ayoyinsu da yin hadin gwiwa bisa taken “Hada hannu don ciyar da zamanantarwa gaba, da gina al’ummar Sin da Afirka mai makomar bai daya”.

 

Mu dawo kan batun “Mallaka” wato “Colonialism” a Turance, wannan kalma ce da ake yawan samu a cikin litattafan tarihi, wadda akasari ke da alaka da tsarin mulkin mallakar kasashen yamma, wadda a halin yanzu wasu kafafen yada labarai da ‘yan siyasa na kasashen yamma suke lakabtawa ayyukan kasar Sin a Afirka cikin shekarun nan. Tambayar ita ce, me ya sa kasashen yamma ke zargin kasar Sin da yin mulkin mallaka a Afirka? Shugaban kasar Burundi Ndayishimiye ya ba da amsar wannan tambayar, inda ya ce: “Lokacin da ‘yan mulkin mallaka da suka yi mulkin mallaka suka ga yadda kasar Sin ke kara karfi da kuma sha’awarta na yin hadin gwiwa da kasashen Afirka, dole tunanin mulkin mallakar da suka yi wa kasashen Afirka ya dawo musu”. Dole ne mu fahimci cewa tsarguwa ce kawai ke sanya kasashen yamma rura wutar kiyayya da adawa da kasar Sin. (Mohammed Yahaya)

Labarai Masu Nasaba

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Tallafawa Majinyata 1000 Da Abinci Da Kuɗi

Next Post

Dalilin Mutuwar Shahararren Ɗan Daban Kano Bayan Wani Artabu

Related

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu
Daga Birnin Sin

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

11 hours ago
Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu
Daga Birnin Sin

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

12 hours ago
Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta
Daga Birnin Sin

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

13 hours ago
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

15 hours ago
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

16 hours ago
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu
Daga Birnin Sin

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

17 hours ago
Next Post
Dalilin Mutuwar Shahararren Ɗan Daban Kano Bayan Wani Artabu

Dalilin Mutuwar Shahararren Ɗan Daban Kano Bayan Wani Artabu

LABARAI MASU NASABA

Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

May 31, 2025
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

May 31, 2025
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

May 31, 2025
Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu

May 30, 2025
Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Ta Jiragen Kasa A Sin Na Iya Kaiwa Sama Da Miliyan 80 Yayin Hutun Bikin Duanwu

May 30, 2025
Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta

May 30, 2025
Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

May 30, 2025
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 30, 2025
Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

May 30, 2025
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

May 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.