• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwa Ce Tsakanin Sin da Afirka Ba Mulkin Mallaka ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

Kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen ba da gudummawa ga ci gaban Afirka ta hanyar ginawa da gyara muhimman ababen more rayuwa kamar madatsun ruwa da tituna da asibitoci, wadanda suka karfafa dunkulewar yankin, da habaka cinikayya da masana’antu. Don haka, yawancin kasashen Afirka suna daraja hadin gwiwarsu da kasar Sin, saboda tana goyon bayan manufofinsu na ci gaba. A fannin kiwon lafiya, tallafin jinya na kasar Sin ya inganta samun damammaki da walwala ga yawancin kasashen Afirka. Haka ma, shirye-shiryen horar da ilimi da fasaha, irin su tallafin karatu da kafa cibiyoyin Confucius da na Luban da dai sauransu sun inganta jarin dan Adam tare da tallafawa ayyukan zamanantar da Afirka.

 

Hadin gwiwar Sin da Afirka ta haifar da nasarori mara misaltuwa wandanda suka rusa ikirarin kafafen yada labaran kasashen yammacin duniya na cewa kasar Sin tana “mallakar” Afirka. Hasali ma, hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka ya zama misalin dangantakar dake tsakanin kasa da kasa bisa daidaito ba tare da mamaya ba, wadda ke nuna sabon salo na sahihin tsarin hadin gwiwar dake tsakanin kasashen duniya, wadda kuma ta ginu bisa mutunta juna da samun moriyar juna. A gun taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka ko FOCAC na shekarar 2024 da za a gudanar daga ranar 4 zuwa ta 6 ga wannan wata, shugabannin bangarorin biyu za su yi musayar ra’ayoyinsu da yin hadin gwiwa bisa taken “Hada hannu don ciyar da zamanantarwa gaba, da gina al’ummar Sin da Afirka mai makomar bai daya”.

 

Mu dawo kan batun “Mallaka” wato “Colonialism” a Turance, wannan kalma ce da ake yawan samu a cikin litattafan tarihi, wadda akasari ke da alaka da tsarin mulkin mallakar kasashen yamma, wadda a halin yanzu wasu kafafen yada labarai da ‘yan siyasa na kasashen yamma suke lakabtawa ayyukan kasar Sin a Afirka cikin shekarun nan. Tambayar ita ce, me ya sa kasashen yamma ke zargin kasar Sin da yin mulkin mallaka a Afirka? Shugaban kasar Burundi Ndayishimiye ya ba da amsar wannan tambayar, inda ya ce: “Lokacin da ‘yan mulkin mallaka da suka yi mulkin mallaka suka ga yadda kasar Sin ke kara karfi da kuma sha’awarta na yin hadin gwiwa da kasashen Afirka, dole tunanin mulkin mallakar da suka yi wa kasashen Afirka ya dawo musu”. Dole ne mu fahimci cewa tsarguwa ce kawai ke sanya kasashen yamma rura wutar kiyayya da adawa da kasar Sin. (Mohammed Yahaya)

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Next Post
Dalilin Mutuwar Shahararren Ɗan Daban Kano Bayan Wani Artabu

Dalilin Mutuwar Shahararren Ɗan Daban Kano Bayan Wani Artabu

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.