ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwa Ce Tsakanin Sin da Afirka Ba Mulkin Mallaka ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Sin

Kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen ba da gudummawa ga ci gaban Afirka ta hanyar ginawa da gyara muhimman ababen more rayuwa kamar madatsun ruwa da tituna da asibitoci, wadanda suka karfafa dunkulewar yankin, da habaka cinikayya da masana’antu. Don haka, yawancin kasashen Afirka suna daraja hadin gwiwarsu da kasar Sin, saboda tana goyon bayan manufofinsu na ci gaba. A fannin kiwon lafiya, tallafin jinya na kasar Sin ya inganta samun damammaki da walwala ga yawancin kasashen Afirka. Haka ma, shirye-shiryen horar da ilimi da fasaha, irin su tallafin karatu da kafa cibiyoyin Confucius da na Luban da dai sauransu sun inganta jarin dan Adam tare da tallafawa ayyukan zamanantar da Afirka.

 

Hadin gwiwar Sin da Afirka ta haifar da nasarori mara misaltuwa wandanda suka rusa ikirarin kafafen yada labaran kasashen yammacin duniya na cewa kasar Sin tana “mallakar” Afirka. Hasali ma, hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka ya zama misalin dangantakar dake tsakanin kasa da kasa bisa daidaito ba tare da mamaya ba, wadda ke nuna sabon salo na sahihin tsarin hadin gwiwar dake tsakanin kasashen duniya, wadda kuma ta ginu bisa mutunta juna da samun moriyar juna. A gun taron koli na dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka ko FOCAC na shekarar 2024 da za a gudanar daga ranar 4 zuwa ta 6 ga wannan wata, shugabannin bangarorin biyu za su yi musayar ra’ayoyinsu da yin hadin gwiwa bisa taken “Hada hannu don ciyar da zamanantarwa gaba, da gina al’ummar Sin da Afirka mai makomar bai daya”.

ADVERTISEMENT

 

Mu dawo kan batun “Mallaka” wato “Colonialism” a Turance, wannan kalma ce da ake yawan samu a cikin litattafan tarihi, wadda akasari ke da alaka da tsarin mulkin mallakar kasashen yamma, wadda a halin yanzu wasu kafafen yada labarai da ‘yan siyasa na kasashen yamma suke lakabtawa ayyukan kasar Sin a Afirka cikin shekarun nan. Tambayar ita ce, me ya sa kasashen yamma ke zargin kasar Sin da yin mulkin mallaka a Afirka? Shugaban kasar Burundi Ndayishimiye ya ba da amsar wannan tambayar, inda ya ce: “Lokacin da ‘yan mulkin mallaka da suka yi mulkin mallaka suka ga yadda kasar Sin ke kara karfi da kuma sha’awarta na yin hadin gwiwa da kasashen Afirka, dole tunanin mulkin mallakar da suka yi wa kasashen Afirka ya dawo musu”. Dole ne mu fahimci cewa tsarguwa ce kawai ke sanya kasashen yamma rura wutar kiyayya da adawa da kasar Sin. (Mohammed Yahaya)

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Dalilin Mutuwar Shahararren Ɗan Daban Kano Bayan Wani Artabu

Dalilin Mutuwar Shahararren Ɗan Daban Kano Bayan Wani Artabu

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.