• Leadership Hausa
Monday, January 30, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwa Tsakanin Matasan Sin Da Afirka Zai Fadada Cin Gajiyar Kasashen Su

by CMG Hausa
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Hadin Gwiwa Tsakanin Matasan Sin Da Afirka Zai Fadada Cin Gajiyar Kasashen Su

Bayan kammalar dandalin matasan Sin da Afirka karo na biyu da aka gudanar a ‘yan kwanakin baya ta kafar bidiyo, masana da masu fashin baki sun nuna gamsuwa da ma’anar dandalin, bisa yadda aka yi amfani da shi wajen yin kira da a karfafa kawance, da hadin gwiwa a fannoni daban daban, domin raya Sin da Afirka bisa juriya da cin moriyar juna yadda ya kamata.

Dandalin wanda kungiyar sada zumunta tsakanin jama’ar kasar Sin da ta kasashen waje ko CPAFFC ta shirya, ya hallara masu ruwa da tsaki a fannin tsara manufofi, da ma’aikatan diflomasiyya, da masana, da dalibai, da wakilai daga kungiyoyin lura da walwalar jama’a, ya jaddada muhimmancin karfafa hadin gwiwa tsakanin matasan Sin da na kasashen Afirka, a matsayin wani ginshiki na kyautata rayuwar bil adama.

  • Xi Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Ilimi Karo Na 16 Na Cibiyoyin Kimiya Na Kasashe Masu Tasowa

Wanda kuma nasarar sa za ta bude wani sabon babin goyon bayan juna tsakanin Sin da kasashen Afirka, musamman da yake batu ake yi na matasa, wadanda Bahaushe kan ce da su “Manyan Gobe”.
Alal hakika, Sin da kasashen Afirka, sun jima suna raya kawance da goyon bayan juna a lokutan yalwa da na tunkarar wahalhalu, kuma a matsayin ta na babbar kasa mai tasowa, Sin bata taba mantawa da abokan huldar ta na kasashen Afirka ba, inda take samar musu da tallafi ciki har da na kiwon lafiya, tare da taimakon samar da manyan ababen more rayuwa, kamar layukan dogo, da manyan hanyoyin mota, da gadoji, da cibiyoyin samar da lantarki, da filayen jiragen sama da sauran su.

La’akari da hakan ne ma, masana da dama ke ganin ko shakka ba bu, idan aka yi amfani da dandalin matasan Sin da Afirka, wajen yaukaka dangantakar sassan biyu, hakan zai kara ingiza cimma manyan nasarori a fannoni daban daban tsakanin sassan biyu, musamman ganin cewa, tuni an samar da manyan manufofin bunkasa hadin gwiwar sassan biyu, karkashin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka, da shawarar nan ta “Ziri Daya Da hanya Daya”.

Don haka dai, akwai bukatar matasan Sin da na kasashen Afirka su kara wucewa gaba wajen fadada kawance, da musaya, da hadin gwiwa tsakanin su, domin cimma kafuwar al’umma guda ta Sin da Afirka, mai makomar bai daya a dukkanin fannoni.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Shawo Kan Amfani Da Karfin Tuwo Da Jami’an Tsaro Ke Yi Kan Fararen Hula

Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

Previous Post

Bagudu Ya Fitar Da Naira Miliyan 30 Don Daukar Nauyin ‘Yan Wasan Kebbi

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Hanyar Abuja Zuwa Kogi

Related

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Shawo Kan Amfani Da Karfin Tuwo Da Jami’an Tsaro Ke Yi Kan Fararen Hula
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Shawo Kan Amfani Da Karfin Tuwo Da Jami’an Tsaro Ke Yi Kan Fararen Hula

54 mins ago
Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 
Daga Birnin Sin

Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

2 hours ago
Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci
Daga Birnin Sin

Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci

3 hours ago
Ban Da Tyre Nichols, Wane Ne mutum Na Gaba Da ’Yan Sandan Amurka Za Su Yi Ajalinsa? 
Daga Birnin Sin

Ban Da Tyre Nichols, Wane Ne mutum Na Gaba Da ’Yan Sandan Amurka Za Su Yi Ajalinsa? 

4 hours ago
Gogewar Kasar Sin A Fannonin Ilimi Da Binciken Kimiyya, Abun Karfafa Gwiwa Ne Ga Kasashen Larabawa 
Daga Birnin Sin

Gogewar Kasar Sin A Fannonin Ilimi Da Binciken Kimiyya, Abun Karfafa Gwiwa Ne Ga Kasashen Larabawa 

5 hours ago
Kasar Sin Ta Tsawaita Wasu Dabarunta Na Kudi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Tsawaita Wasu Dabarunta Na Kudi

6 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Bukaci N40m Kudin Fansar Yara 20 Da Suka Sace A Neja

'Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Hanyar Abuja Zuwa Kogi

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Shawo Kan Amfani Da Karfin Tuwo Da Jami’an Tsaro Ke Yi Kan Fararen Hula

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Shawo Kan Amfani Da Karfin Tuwo Da Jami’an Tsaro Ke Yi Kan Fararen Hula

January 30, 2023
Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

Sin: An Samu Karuwar Sayayyar Amfanin Gona Ta Yanar Gizo A 2022 

January 30, 2023
Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci

Wannan Sabuwar Tashar Jirgin Ruwa Ta Shaida Wani Tunani Mai Muhimmanci

January 30, 2023
Ban Da Tyre Nichols, Wane Ne mutum Na Gaba Da ’Yan Sandan Amurka Za Su Yi Ajalinsa? 

Ban Da Tyre Nichols, Wane Ne mutum Na Gaba Da ’Yan Sandan Amurka Za Su Yi Ajalinsa? 

January 30, 2023
Gogewar Kasar Sin A Fannonin Ilimi Da Binciken Kimiyya, Abun Karfafa Gwiwa Ne Ga Kasashen Larabawa 

Gogewar Kasar Sin A Fannonin Ilimi Da Binciken Kimiyya, Abun Karfafa Gwiwa Ne Ga Kasashen Larabawa 

January 30, 2023
Babban Kwamatin Ayyuka Na Jam’iyyar PDP Na kasa Ya Gana Da ‘Yan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar

‘Yan Majalisar Tarayya 3 Na Jam’iyyar APC Sun Koma Jam’iyyar PDP A Jihar Katsina

January 30, 2023
Kasar Sin Ta Tsawaita Wasu Dabarunta Na Kudi

Kasar Sin Ta Tsawaita Wasu Dabarunta Na Kudi

January 30, 2023
DSS Ta Kama Wasu Ma’aikatan Banki Masu Hada-hadar Sayar Da Sabbin Kudaden Naira

DSS Ta Kama Wasu Ma’aikatan Banki Masu Hada-hadar Sayar Da Sabbin Kudaden Naira

January 30, 2023
Tsohon Firaministan Kenya, Odinga, Ya Iso Nijeriya Don Halartar Taron LEADERSHIP Na 14

Tsohon Firaministan Kenya, Odinga, Ya Iso Nijeriya Don Halartar Taron LEADERSHIP Na 14

January 30, 2023
Jirgin Kasan Kaduna-Abuja Ya Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Bayan Hatsarin Da Ya Yi

Jirgin Kasan Kaduna-Abuja Ya Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Bayan Hatsarin Da Ya Yi

January 30, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.