• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ta Fannin Sabbin Makamashi Ya Samar Da Mafita Ta Tabbatar Da Ci Gaba Mai Dorewa A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ta Fannin Sabbin Makamashi Ya Samar Da Mafita Ta Tabbatar Da Ci Gaba Mai Dorewa A Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Yanzu ba mu damuwa da ruwan sha da lantarki, muna godiya ga aminanmu Sinawa wadanda suka taimaka mana wajen gina tashoshin samar da wutar lantarki da kafa fitilu da haka rijiyoyi.” Shugaban kauyen Koniobla, malam Jean Doumbia ne ya fadi haka cikin farin ciki, lokacin da ya ga sabbin fitilu na haskaka titi da ma hasumiyar samar da ruwa da aka gina a kauyen. 

 

Kasar Mali ta dade tana fama da matsalar karancin wutar lantarki, inda kauyukanta da suka samu damar yin amfani da lantarki bai kai kaso 20% ba. Kauyen Koniobla yana kudu maso gabashin birnin Bamako, kuma kusan ba a samun lantarki a kauyen, inda mazauna kauyen su kan shiga dogon layi don su debo ruwa daga wasu rijiyoyi da ke cikn kauyen. Amma hakan ya sauya bayan da kamfanin kasar Sin ya kammala shirin samar da wutar lantarki da zafin rana a wasu kauyuka biyu da suka hada da Koniobla da Karan na kasar ta Mali a bara, inda aka kafa tsarin samar da wuta da zafin rana da ma tsarin fitilun titi da tsarin samar da ruwan famfo da zafin rana da sauransu, wadanda suka amfani al’ummar wurin sama da su dubu 10.

  • Me Ya Sa Dandalin FOCAC Ke Samun Karbuwa A Tsakanin Al’ummar Nahiyar Afrika?
  • Xi: Sin Da Afirka Sun Zamo Sassa Na Farko Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya

Daga nan, ko da an shiga duhun dare, ana samun hasken fitilu a kauyukan, kuma ko yaushe ana iya samun ruwa mai tsabta da famfo da ke aiki da lantarki, har ma karin magidanta na kauyen suka sayi talabijin.

 

Labarai Masu Nasaba

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Kamar yadda Mali take, matsalar karancin makamashi na yi wa bunkasuwar akasarin sassan Afirka tarnaki. Duk da haka, Allah ya albarkaci Afirka da makamashi masu tsabta, irinsu makamashin iska da na rana, wanda hakan ya samar da dama ta warware matsalar. Abin da ya faru a kauyen Koniobla, ya shaida yadda Sin da kasashen Afirka suke hadin gwiwa da juna a wannan fanni tare da haifar da nasara.

 

A hakika, bisa tsarin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da ma shawarar ziri daya da hanya daya, kasar Sin ta aiwatar da daruruwan shirye-shirye na samar da makamashi masu tsabta a kasashen Afirka. Misali a Nijeriya, tashar ruwa ta samar da wuta ta Zungeru da kamfanin kasar Sin ya gina ya kasance irinta mafi girma a kasar, wanda ke samar da lantarki da zai iya biyan bukatun birane masu girman Abuja guda biyu, sai kuma a bara, aka kaddamar da motocin safa masu aiki da lantarki na farko da kamfanin kasar Sin ya kera a birnin Lagos…

 

Kasancewar dukkansu kasashe masu tasowa, kasar Sin ta san tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba hanya ce daya tilo da za ta daidaita matsalar sauyin yanayi, da kuma tabbatar da dauwamammen ci gaba, haka kuma ta san yadda kasashen Afirka ke matukar fatan ganin samun bunkasuwarsu, da ma kalubalen da suke fuskanta, don haka take son raba nasarorin da ta cimma a fannin tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba.

 

Yanzu haka taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na gudana a birnin Beijing, kuma batun tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba na daya daga cikin batutuwan da suka fi daukar hankalin mahalarta taron. Muna da imani kan cewa, Sin da kasashen Afirka za su tsara sabbin shirye-shiryen hadin gwiwa a wannan fanni, don tabbatar da dauwamammen ci gaba a kasashen Afirka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

UNECA: Sin Na Tallafawa Afirka Sauyi Zuwa Makamashi Mai Tsabta Ta Hanyar Shigar Da EV

Next Post

An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu

Related

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

4 hours ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

3 days ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

5 days ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

6 days ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

1 week ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

2 weeks ago
Next Post
An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu

An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.