ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ta Fannin Sabbin Makamashi Ya Samar Da Mafita Ta Tabbatar Da Ci Gaba Mai Dorewa A Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Afirka

“Yanzu ba mu damuwa da ruwan sha da lantarki, muna godiya ga aminanmu Sinawa wadanda suka taimaka mana wajen gina tashoshin samar da wutar lantarki da kafa fitilu da haka rijiyoyi.” Shugaban kauyen Koniobla, malam Jean Doumbia ne ya fadi haka cikin farin ciki, lokacin da ya ga sabbin fitilu na haskaka titi da ma hasumiyar samar da ruwa da aka gina a kauyen. 

 

Kasar Mali ta dade tana fama da matsalar karancin wutar lantarki, inda kauyukanta da suka samu damar yin amfani da lantarki bai kai kaso 20% ba. Kauyen Koniobla yana kudu maso gabashin birnin Bamako, kuma kusan ba a samun lantarki a kauyen, inda mazauna kauyen su kan shiga dogon layi don su debo ruwa daga wasu rijiyoyi da ke cikn kauyen. Amma hakan ya sauya bayan da kamfanin kasar Sin ya kammala shirin samar da wutar lantarki da zafin rana a wasu kauyuka biyu da suka hada da Koniobla da Karan na kasar ta Mali a bara, inda aka kafa tsarin samar da wuta da zafin rana da ma tsarin fitilun titi da tsarin samar da ruwan famfo da zafin rana da sauransu, wadanda suka amfani al’ummar wurin sama da su dubu 10.

ADVERTISEMENT
  • Me Ya Sa Dandalin FOCAC Ke Samun Karbuwa A Tsakanin Al’ummar Nahiyar Afrika?
  • Xi: Sin Da Afirka Sun Zamo Sassa Na Farko Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya

Daga nan, ko da an shiga duhun dare, ana samun hasken fitilu a kauyukan, kuma ko yaushe ana iya samun ruwa mai tsabta da famfo da ke aiki da lantarki, har ma karin magidanta na kauyen suka sayi talabijin.

 

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Kamar yadda Mali take, matsalar karancin makamashi na yi wa bunkasuwar akasarin sassan Afirka tarnaki. Duk da haka, Allah ya albarkaci Afirka da makamashi masu tsabta, irinsu makamashin iska da na rana, wanda hakan ya samar da dama ta warware matsalar. Abin da ya faru a kauyen Koniobla, ya shaida yadda Sin da kasashen Afirka suke hadin gwiwa da juna a wannan fanni tare da haifar da nasara.

 

A hakika, bisa tsarin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka da ma shawarar ziri daya da hanya daya, kasar Sin ta aiwatar da daruruwan shirye-shirye na samar da makamashi masu tsabta a kasashen Afirka. Misali a Nijeriya, tashar ruwa ta samar da wuta ta Zungeru da kamfanin kasar Sin ya gina ya kasance irinta mafi girma a kasar, wanda ke samar da lantarki da zai iya biyan bukatun birane masu girman Abuja guda biyu, sai kuma a bara, aka kaddamar da motocin safa masu aiki da lantarki na farko da kamfanin kasar Sin ya kera a birnin Lagos…

 

Kasancewar dukkansu kasashe masu tasowa, kasar Sin ta san tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba hanya ce daya tilo da za ta daidaita matsalar sauyin yanayi, da kuma tabbatar da dauwamammen ci gaba, haka kuma ta san yadda kasashen Afirka ke matukar fatan ganin samun bunkasuwarsu, da ma kalubalen da suke fuskanta, don haka take son raba nasarorin da ta cimma a fannin tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba.

 

Yanzu haka taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na gudana a birnin Beijing, kuma batun tabbatar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba na daya daga cikin batutuwan da suka fi daukar hankalin mahalarta taron. Muna da imani kan cewa, Sin da kasashen Afirka za su tsara sabbin shirye-shiryen hadin gwiwa a wannan fanni, don tabbatar da dauwamammen ci gaba a kasashen Afirka.

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu

An Kaddamar Da Shirin “Afirka a Cikin Fina-Finai” Zagaye Na Biyu

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.