• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
in Ra'ayi Riga
0
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashen Afirka da dama ciki har da Najeriya sun dade suna fama da matsalar karancin wutar lantarki, sai dai wani rahoto na baya-bayan nan da kungiyar Ember mai nazarin makamashi ta duniya ta fitar, ya nuna cewa wannan yanayi yana canzawa.

 

Ta la’akari da yadda kasar Sin take samar da kaso 80% na allunan sola masu samar da wutar lantarki daga hasken rana na duniya, rahoton ya yi nazari a kan alkaluman shigar da allunan sola daga kasar Sin zuwa kasashen Afirka, tsakanin watan Yulin 2024 zuwa watan Yunin 2025, inda sakamako ya nuna cewa:

1. Yawan allunan sola da aka shigar da su Afirka ya karu da kaso 60%;

2. Karuwar shigar da allunan sola ta shafi kusan dukkan kasashen Afirka, inda jimillar wasu kasashe 20 a fannin ta kai matsayin koli a tarihi;

Labarai Masu Nasaba

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

3. Karuwar allunan sola ta samar da damar samun karin wutar lantarki, inda ake sa ran samun karuwar wutar lantarki da za ta kai fiye da kaso 5% a wasu kasashe 16 dake nahiyar Afirka.

Tambaya ita ce: me ya sa allunan solan kasar Sin samun karbuwa a Afirka? Domin suna da araha, gami da inganci.

Kamar yadda muka sani, ana sayar da allon sola mai karfin watt 420 kan farashin kusan dalar Amurka 60 a Najeriya, kuma yana iya samar da wutar lantarki na kWh 550 a duk shekara. Sai dai idan za mu ci gaba da samar da wutar lantarki ta janareta mai amfani da man dizal, kamar yadda aka saba yi, to, a farashin man dizal na yanzu na dala 0.66 kan lita daya, man dizal na dala 60 zai samar da kWh 275 na wutar lantarki ne kawai. Wannan yana nufin cewa, ta hanyar amfani da allunan sola, kudin da aka yi tsiminsa zai biya kudin da aka kashe cikin watanni shida kacal. Ba a ma maganar saukin amfani, da damar biyan bukatar kare muhalli da allon ke da su.

Sa’an nan, na san tabbas ana mamakin yadda allunan sola, da suka yi tsada a baya, suka yi araha a yanzu. Wannan ya faru ne saboda manufar kasar Sin ta bunkasa makamashi mai tsafta, ta kawo sauye-sauye ga yanayin kasuwar makamashi ta duniya.

Tsakanin shekarar 2021 da ta 2025, kasar Sin ta gina tsarin amfani da makamashi da ake iya sabuntawa mafi girma da saurin ci gaba a duniya, wanda ya sa karfin kasar na samar da wutar lantarki ta makamashin da ake iya sabuntawa, ya karu daga kaso 40% zuwa kimanin kaso 60%. A sa’i daya kuma, kasar Sin ta zama kasa ta farko wajen fitar da fasahohin makamashi mai tsafta a duniya, wadda take fitar da na’urorin samar da wutar lanarki daga hasken rana da iska zuwa kasashe da yankuna sama da 200. Ci gaban fasaha na kasar Sin da kuma karfinta na samar da dimbin kayayyaki cikin sauri sun tabbatar da rahusar kayayyakinta, da ba su damar samun karbuwa a tsakanin al’ummun kasashe daban daban. Bisa wani bincike da shafin yanar gizo na Carbon Brief da ke Burtaniya ya yi, cikin shekaru goma da suka gabata, kasar Sin ta taimaka wajen rage matsakaicin kudin da ake kashewa domin samar da wutar lantarki daga hasken rana da kaso 80%.

Albarkacin cudanya da kasuwanci da ake yi tsakanin Sin da Afirka, sannu a hankali sararin samaniyar Afirka na kara haskakawa da dare. Amma wannan mafari ne kawai. Saboda a bangare guda, nahiyar Afirka ce ke da kaso 40% na zafin hasken rana a duniya, da kaso 32% na karfin iska, da kaso 12% na karfin ruwa. A daya hannun kuma, neman ci gaban tattalin arziki da kare muhalli a lokaci guda, wani muhimmin jigo ne a hadin gwiwar Sin da Afirka. A cikin ‘yan shekarun nan, kasar Sin ta aiwatar da daruruwan ayyuka masu alaka da makamashi mai tsafta, da aikin raya tattalin arziki ta hanyar kare muhalli a Afirka. Ta hanyar musayar fasahohi, da hadin gwiwa kan wasu ayyuka, da samar da tallafi a bangaren hada-hadar kudi, kasar Sin na kara zurfafa hadin gwiwar dake tsakanin ta da kasashen Afirka a fannin raya makamashi mai tsafta. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

Next Post

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

Related

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

11 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

2 days ago
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

1 week ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

2 weeks ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

2 weeks ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

2 weeks ago
Next Post
Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.