• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Turai Zai Yaukaka Daidaiton Dangantaka

byCGTN Hausa
1 year ago
Turai

Ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ke gudanarwa a kasashen Faransa, da Serbia, da Hungary, ta kasance muhimmin matakin yaukaka dangantakar diflomasiyyar bangarorin biyu.

Kasar Sin da kasashen Turai karkashin jagorancin kungiyar EU, muhimman bangarori ne biyu dake ingiza manufar samar da tasirin fada-a-ji daga bangarori daban daban, kuma sassan biyu na matukar goyon bayan dunkulewar duniya, a bangare daya kuma, sun kasance bangarori masu rungumar mabanbantan wayewar kai a duniya. Don hake ne ma masharhanta da dama ke kallon alakar Sin da Turai a matsayin mai da matukar muhimmanci wajen saita akalar ci gaban duniya baki daya.

  • An Gabatar Da Shirin Talabijin Mai Suna Labarun Da Xi Jinping Ya Fi So A Hungary
  • Shugaba Xi: Har Kullum Sin Da Hungary Na Kallon Alakarsu Daga Mahanga Mai Fadi Da Wa’adi Mai Tsawo

Masu fashin baki na ganin cewa, Sin da kasashen tarayyar Turai ba su da manyan banbance-banbancen neman cimma moriya, ko sabani ta fuskar siyasar yankunan su. Kaza lika, batutuwan da suke dunkule sassan biyu wuri guda, sun rinjayi banbance-banbancensu. Hakan ne kuma ya sa har kullum suke ta kokarin yaukaka alakar su, ta yadda za su ci gaba da kasancewa sahihan kawaye abun koyi, su kuma ci gaba da yin hadin gwiwa, da cimma moriya tare a yanzu da ma nan gaba.

A bangarenta, a ko da yaushe kasar Sin na daukar tarayyar Turai a matsayin muhimmin karfi dake da tasiri a harkokin kasa da kasa, tana kuma sanya batun raya dangantakarta da EU a sahun gaba cikin harkokin diflomasiyyarta.

Bisa hakan ne ma a bazarar shekarar 2014, shugaba Xi ya ziyarci helkwatar kungiyar EU, inda a lokacin ya gabatar da shawarar hada karfi da karfe tsakanin kasarsa da EU, a fannonin wanzar da zaman lafiya, da samar da ci gaba, da gudanar da sauye-sauye, da bunkasa wayewar kai. Har yanzu kuma wannan kuduri bai sauya ba, yana kuma ci gaba da zama alkiblar raya dangantakar sassan biyu a halin da ake ciki yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Yayin da duniya ke kara tsunduma cikin hali na rashin tabbas, da rigingimu nan da can, yana da kyau Sin da EU su wanzar da tattaunawa ta kut da kut, su kuma mayar da hankali ga hadin gwiwar cimma moriyar juna, daga fannin ingiza ci gaban bangarorin biyu zuwa tunkarar kalubalolin dake addabar duniya baki daya.

Tabbatattun shaidu sun nuna cewa, muddin Sin da EU sun yi aiki tare wajen saita alkiblar da za su bi domin bunkasa kan su, ko shakka babu hakan zai iya kai su ga cimma burikan da suka sanya gaba, tare da haifarwa alummun su da tarin alherai.

A halin da ake ciki, Sin na kan gaba a jerin sassa mafiya muhimmanci ga Turai a fannin hada-hadar cinikayya. Duk da tafiyar hawainiya da tattalin arzikin duniya ke yi a yanzu, a shekarar bara, jimillar darajar cinikayya tsakanin Sin da EU ta kai dala biliyan 783. Kaza lika Sin na yiwa Turai maraba a fannonin cin gajiyar hadin gwiwar kasuwanci, da raya kimiyya da fasaha, da bunkasa hidimomin sarrafa hajojin masanaantu da rarraba su ga sassan duniya, ta yadda sassan biyu za su ci gajiyar bai daya, da samun nasara da walwala tare.

Ko shakka babu sannu a hankali, hadin gwiwar Sin da Turai na bunkasa, musamman ma a fannonin da duniya ke mayar da hankali yanzu a kansu, kamar tattalin arziki na dijital, da bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba, da cin gajiya daga sabbin makamashi, da kirkirarriyar basira.

Bunkasar Sin wata dama ce ga EU, kana daidaita kawancen sassan biyu zai taimaka matuka wajen shawo kan kalubale da EU ke fuskanta. A halin da ake ciki, karin sassan Turai na dada fahimtar muhimmancin hada gwiwa da Sin, wajen magance matsalolin makamashi, da hauhawar farashin hajoji da EU ke fuskanta, a daya bangaren dangantakar sassan biyu za ta kyautata takara mai tsafta tsakaninsu, da haifar da gajiya ga Sin da turai da ma duniya baki daya. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
Lokaci Ya Yi Da Za A Kara Dakon Zumunci A Tsakanin Sin Da Serbia

Lokaci Ya Yi Da Za A Kara Dakon Zumunci A Tsakanin Sin Da Serbia

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version