• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hadin Gwiwar Sin Da Turai Zai Yaukaka Daidaiton Dangantaka

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Hadin Gwiwar Sin Da Turai Zai Yaukaka Daidaiton Dangantaka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ke gudanarwa a kasashen Faransa, da Serbia, da Hungary, ta kasance muhimmin matakin yaukaka dangantakar diflomasiyyar bangarorin biyu.

Kasar Sin da kasashen Turai karkashin jagorancin kungiyar EU, muhimman bangarori ne biyu dake ingiza manufar samar da tasirin fada-a-ji daga bangarori daban daban, kuma sassan biyu na matukar goyon bayan dunkulewar duniya, a bangare daya kuma, sun kasance bangarori masu rungumar mabanbantan wayewar kai a duniya. Don hake ne ma masharhanta da dama ke kallon alakar Sin da Turai a matsayin mai da matukar muhimmanci wajen saita akalar ci gaban duniya baki daya.

  • An Gabatar Da Shirin Talabijin Mai Suna Labarun Da Xi Jinping Ya Fi So A Hungary
  • Shugaba Xi: Har Kullum Sin Da Hungary Na Kallon Alakarsu Daga Mahanga Mai Fadi Da Wa’adi Mai Tsawo

Masu fashin baki na ganin cewa, Sin da kasashen tarayyar Turai ba su da manyan banbance-banbancen neman cimma moriya, ko sabani ta fuskar siyasar yankunan su. Kaza lika, batutuwan da suke dunkule sassan biyu wuri guda, sun rinjayi banbance-banbancensu. Hakan ne kuma ya sa har kullum suke ta kokarin yaukaka alakar su, ta yadda za su ci gaba da kasancewa sahihan kawaye abun koyi, su kuma ci gaba da yin hadin gwiwa, da cimma moriya tare a yanzu da ma nan gaba.

A bangarenta, a ko da yaushe kasar Sin na daukar tarayyar Turai a matsayin muhimmin karfi dake da tasiri a harkokin kasa da kasa, tana kuma sanya batun raya dangantakarta da EU a sahun gaba cikin harkokin diflomasiyyarta.

Bisa hakan ne ma a bazarar shekarar 2014, shugaba Xi ya ziyarci helkwatar kungiyar EU, inda a lokacin ya gabatar da shawarar hada karfi da karfe tsakanin kasarsa da EU, a fannonin wanzar da zaman lafiya, da samar da ci gaba, da gudanar da sauye-sauye, da bunkasa wayewar kai. Har yanzu kuma wannan kuduri bai sauya ba, yana kuma ci gaba da zama alkiblar raya dangantakar sassan biyu a halin da ake ciki yanzu.

Labarai Masu Nasaba

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

Yayin da duniya ke kara tsunduma cikin hali na rashin tabbas, da rigingimu nan da can, yana da kyau Sin da EU su wanzar da tattaunawa ta kut da kut, su kuma mayar da hankali ga hadin gwiwar cimma moriyar juna, daga fannin ingiza ci gaban bangarorin biyu zuwa tunkarar kalubalolin dake addabar duniya baki daya.

Tabbatattun shaidu sun nuna cewa, muddin Sin da EU sun yi aiki tare wajen saita alkiblar da za su bi domin bunkasa kan su, ko shakka babu hakan zai iya kai su ga cimma burikan da suka sanya gaba, tare da haifarwa alummun su da tarin alherai.

A halin da ake ciki, Sin na kan gaba a jerin sassa mafiya muhimmanci ga Turai a fannin hada-hadar cinikayya. Duk da tafiyar hawainiya da tattalin arzikin duniya ke yi a yanzu, a shekarar bara, jimillar darajar cinikayya tsakanin Sin da EU ta kai dala biliyan 783. Kaza lika Sin na yiwa Turai maraba a fannonin cin gajiyar hadin gwiwar kasuwanci, da raya kimiyya da fasaha, da bunkasa hidimomin sarrafa hajojin masanaantu da rarraba su ga sassan duniya, ta yadda sassan biyu za su ci gajiyar bai daya, da samun nasara da walwala tare.

Ko shakka babu sannu a hankali, hadin gwiwar Sin da Turai na bunkasa, musamman ma a fannonin da duniya ke mayar da hankali yanzu a kansu, kamar tattalin arziki na dijital, da bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba, da cin gajiya daga sabbin makamashi, da kirkirarriyar basira.

Bunkasar Sin wata dama ce ga EU, kana daidaita kawancen sassan biyu zai taimaka matuka wajen shawo kan kalubale da EU ke fuskanta. A halin da ake ciki, karin sassan Turai na dada fahimtar muhimmancin hada gwiwa da Sin, wajen magance matsalolin makamashi, da hauhawar farashin hajoji da EU ke fuskanta, a daya bangaren dangantakar sassan biyu za ta kyautata takara mai tsafta tsakaninsu, da haifar da gajiya ga Sin da turai da ma duniya baki daya. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Sin da AfirkaEUHungaryTarayyar Turai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwastam ta Mika Jabun Dalar Amurka Da Jirage Marasa Matuka 148 Da Ta Kwace Ga EFCC Da Sojoji

Next Post

Lokaci Ya Yi Da Za A Kara Dakon Zumunci A Tsakanin Sin Da Serbia

Related

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

16 minutes ago
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2
Daga Birnin Sin

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

1 hour ago
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

1 hour ago
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

19 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

20 hours ago
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

20 hours ago
Next Post
Lokaci Ya Yi Da Za A Kara Dakon Zumunci A Tsakanin Sin Da Serbia

Lokaci Ya Yi Da Za A Kara Dakon Zumunci A Tsakanin Sin Da Serbia

LABARAI MASU NASABA

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

June 27, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

June 27, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

June 27, 2025
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

June 27, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

June 27, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.