• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin 2023: Alhazan Nijeriya 14 Sun Rasu A Saudiyya A Aikin Hajin Bana

by Muhammad
2 years ago
Hajjin 2023

Hukumar Alhazai ta Nijeriya NAHCON, ta bayyana cewa Alhazan Nijeriya 14 sun rasu a kasar Saudiyya daga fara gudanar da aikin hajjin na shekarar 2023 zuwa yanzu.

Shugaban kula da sashen aiyuka kuma shugaban kungiyar likitocin NAHCON na Nijeriya Dr. Usman Galadima, ne ya bayyana haka a wani taro da aka gudanar bayan Arafat da masu ruwa da tsaki a ranar Lahadi a birnin Makkah na kasar Saudiyya.

  • Saudiyya Ta Tsare Mutum 17,000 Da Suka Yi Yunkurin Hajji Ba Tare Da Izini Ba
  • Hajj 2023: NAHCON Ta Cancanci Yabo Da Jinjina Ba Kushe Ba – Almakura

Galadima ya bayyana cewa mahajjata bakwai sun rasu kafin Arafat, shida kuma sun rasu a cikin kwanaki biyar na Mashair (manyan ranakun aikin Hajji) sannan karin mutum daya ya rasu bayan Arafat.

“Mun sami rahoton mutuwar mutane shida a Mashair, hudu sun mutu a Arafat, sauran biyun kuma sun mutu a Mina. Tuni mun rasa mahajjata bakwai kafin Arafat kuma a yanzu haka an sanar da ni cewa mun rasa wani alhaji. Wannan ya kawo adadin wadanda suka mutu zuwa 14.

“Yawan mace-mace yayi kama da na 2019,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Ya kuma bayyana cewa, tawagar likitocin ta samu rahoton bullar cuta ga wasu Alhazai guda uku a lokacin aikin hajji kuma nan da nan aka kwashe alhazan da suka kamu da cutar don yi musu rigakafin kamuwa da cutar.

Galadima ya kuma bayyana cewa, tawagar ta samu rahotan haifuwa biyu a lokacin aikin hajji a Mina, Arafat da Muzdalifah, inda ya kara da cewa daya daga cikin mata masu juna biyu ta haihu a kan hanya, yayin da ta biyu kuma a asibiti.

Ya kuma jaddada bukatar yin cikakken binciken likitocin kafin aikin hajji tare da bayar da takardar shaidar lafiya mai inganci.

Ya kuma ce ya kamata a hana tsofaffin alhazai da masu fama da rashin lafiya shiga wurin jifan shaidan a Jamrat saboda damuwar da ke tattare da hakan.

A nasa jawabin shugaban hukumar ta NAHCON, Alhaji Goni Sanda, ya bayyana cewa za a fara jigilar maniyyata zuwa Nijeriya ne a ranar Talata 4 ga watan Yuli.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
Manyan Labarai

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 7 Da Ceto Wani Mutum A Afganistan

'Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 7 Da Ceto Wani Mutum A Afganistan

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.