• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin 2023: Alhazan Nijeriya 14 Sun Rasu A Saudiyya A Aikin Hajin Bana

by Muhammad
2 years ago
Hajjin 2023

Hukumar Alhazai ta Nijeriya NAHCON, ta bayyana cewa Alhazan Nijeriya 14 sun rasu a kasar Saudiyya daga fara gudanar da aikin hajjin na shekarar 2023 zuwa yanzu.

Shugaban kula da sashen aiyuka kuma shugaban kungiyar likitocin NAHCON na Nijeriya Dr. Usman Galadima, ne ya bayyana haka a wani taro da aka gudanar bayan Arafat da masu ruwa da tsaki a ranar Lahadi a birnin Makkah na kasar Saudiyya.

  • Saudiyya Ta Tsare Mutum 17,000 Da Suka Yi Yunkurin Hajji Ba Tare Da Izini Ba
  • Hajj 2023: NAHCON Ta Cancanci Yabo Da Jinjina Ba Kushe Ba – Almakura

Galadima ya bayyana cewa mahajjata bakwai sun rasu kafin Arafat, shida kuma sun rasu a cikin kwanaki biyar na Mashair (manyan ranakun aikin Hajji) sannan karin mutum daya ya rasu bayan Arafat.

“Mun sami rahoton mutuwar mutane shida a Mashair, hudu sun mutu a Arafat, sauran biyun kuma sun mutu a Mina. Tuni mun rasa mahajjata bakwai kafin Arafat kuma a yanzu haka an sanar da ni cewa mun rasa wani alhaji. Wannan ya kawo adadin wadanda suka mutu zuwa 14.

“Yawan mace-mace yayi kama da na 2019,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

Ya kuma bayyana cewa, tawagar likitocin ta samu rahoton bullar cuta ga wasu Alhazai guda uku a lokacin aikin hajji kuma nan da nan aka kwashe alhazan da suka kamu da cutar don yi musu rigakafin kamuwa da cutar.

Galadima ya kuma bayyana cewa, tawagar ta samu rahotan haifuwa biyu a lokacin aikin hajji a Mina, Arafat da Muzdalifah, inda ya kara da cewa daya daga cikin mata masu juna biyu ta haihu a kan hanya, yayin da ta biyu kuma a asibiti.

Ya kuma jaddada bukatar yin cikakken binciken likitocin kafin aikin hajji tare da bayar da takardar shaidar lafiya mai inganci.

Ya kuma ce ya kamata a hana tsofaffin alhazai da masu fama da rashin lafiya shiga wurin jifan shaidan a Jamrat saboda damuwar da ke tattare da hakan.

A nasa jawabin shugaban hukumar ta NAHCON, Alhaji Goni Sanda, ya bayyana cewa za a fara jigilar maniyyata zuwa Nijeriya ne a ranar Talata 4 ga watan Yuli.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Gwamna Yusuf
Labarai

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
Sabbin Ministoci
Labarai

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 7 Da Ceto Wani Mutum A Afganistan

'Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 7 Da Ceto Wani Mutum A Afganistan

LABARAI MASU NASABA

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.