• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin 2024: NAHCON Za Ta Sabunta Ka’idojin Ciyar Da Alhazai Da Masaukansu

by Khalid Idris Doya
2 years ago
NAHCON

Domin kyautata gudanar da aikin hajji da kuma saukaka wa maniyyata, Hukumar Kula da Jin Dadin Alhazai ta Kasa (NAHCON), za ta sabunta ka’idojin ciyar da alhazai da masaukansu a kasa mai tsarki.

Mukaddashin Shugaban NAHCON, Malam Jalal Ahmad Arabi, ya shaida hakan a ranar Talata, yayin da yake kaddamar da kwamitin da za su sake duba ka’idojin masaukan alhazan da masu aikin dafa musu abinci.
Arabi ya kara da cewa, sake nazartar ka’idojin da ake bi a kan ciyar da alhazan da masaukansu, zai taimaka sosai wajen inganta aikin hidimta wa Alhazan Nijeriya tare da kyautata jin dadi da walwalarsu.

  • Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Kwamitin Mutum 8 Don Inganta Harkokin Aikin Hajjin 2024
  • Kamata Ya Yi Kasashe Masu Ci Gaba Sun Cika Alkawarin Da Suka Yi Na Samar Da Kudaden Taimakawa Kasashe Masu Tasowa Wajen Tinkarar Sauyin Yanayi

A karshe, ya mika wa kwamitin kundin tsarin dokar da zimmar duba hanyoyin da suka dace, domin yin garanbawul ga wuraren da ake da bukatar yin gyara, saboda kwalliya ta biya kudin sabulu na kyautata walwala da jin dadin alhazan yayin da suke can Kasar Saudiyya.

A cewarsa, akwai bukatar yin garanbawul ga tsarin ayyukan a hidimar aikin hajji, domin tafiya daidai da tsarin zamani wadda duniya ke kai a halin yanzu.

“Abun da muke yi yanzu shi ne, duba hanyoyin da suka dace domin inganta al’amura, kamar yadda take gudana a wasu sassan duniya, sannan muna bukatar kwarin guiwa da kuzarin da zai kyautata mana wadannan lamura namu. Har ila yau, akwai bukatar mu inganta hanyoyinmu, domin yin gogayya da kasashen duniya,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

Wakazalika, Shugaba na NAHCON ya bukaci kwamitin ya mayar da hankali wajen gudanar da ayyukan da aka ba shi, yana mai nanata musu cewa, aikin nasu na da matukar muhimmanci; don haka dole su mayar da hankali wajen yin abubuwan da suka dace, domin kyautata lamuran da suka shafi abincin alhazai da kuma masaukinsu a hajjin 2024 da ke tafe.

Yayin da yake nuna kwarin guiwarsa na cewa, kwamitin gabatar da shawarwari masu nagarta wadanda za a amfana da su, Arabi ya shaida cewa, kwamitin na da damar fadada ayyukansu ta yadda za su kawo shawarwari masu alfanu da ma’ana.

Idan ba a manta ba, a shekarar 2023 yayin gudanar da aikin hajji a kasa mai tsarki, Alhazan Nijeriya sun yi ta faman korafin matsalar masauki da ba su abinci mara inganci, wanda suka danganta hakan da kamfanin da aka dora wa alhakin ba su abincin da samar musu da masaukai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
Ba Za A Cimma Wannan Yarjejeniya Ba Tare Da Taimakon Sin Ba

Ba Za A Cimma Wannan Yarjejeniya Ba Tare Da Taimakon Sin Ba

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.