ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin 2024: NAHCON Za Ta Sabunta Ka’idojin Ciyar Da Alhazai Da Masaukansu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
NAHCON

Domin kyautata gudanar da aikin hajji da kuma saukaka wa maniyyata, Hukumar Kula da Jin Dadin Alhazai ta Kasa (NAHCON), za ta sabunta ka’idojin ciyar da alhazai da masaukansu a kasa mai tsarki.

Mukaddashin Shugaban NAHCON, Malam Jalal Ahmad Arabi, ya shaida hakan a ranar Talata, yayin da yake kaddamar da kwamitin da za su sake duba ka’idojin masaukan alhazan da masu aikin dafa musu abinci.
Arabi ya kara da cewa, sake nazartar ka’idojin da ake bi a kan ciyar da alhazan da masaukansu, zai taimaka sosai wajen inganta aikin hidimta wa Alhazan Nijeriya tare da kyautata jin dadi da walwalarsu.

  • Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Kwamitin Mutum 8 Don Inganta Harkokin Aikin Hajjin 2024
  • Kamata Ya Yi Kasashe Masu Ci Gaba Sun Cika Alkawarin Da Suka Yi Na Samar Da Kudaden Taimakawa Kasashe Masu Tasowa Wajen Tinkarar Sauyin Yanayi

A karshe, ya mika wa kwamitin kundin tsarin dokar da zimmar duba hanyoyin da suka dace, domin yin garanbawul ga wuraren da ake da bukatar yin gyara, saboda kwalliya ta biya kudin sabulu na kyautata walwala da jin dadin alhazan yayin da suke can Kasar Saudiyya.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, akwai bukatar yin garanbawul ga tsarin ayyukan a hidimar aikin hajji, domin tafiya daidai da tsarin zamani wadda duniya ke kai a halin yanzu.

“Abun da muke yi yanzu shi ne, duba hanyoyin da suka dace domin inganta al’amura, kamar yadda take gudana a wasu sassan duniya, sannan muna bukatar kwarin guiwa da kuzarin da zai kyautata mana wadannan lamura namu. Har ila yau, akwai bukatar mu inganta hanyoyinmu, domin yin gogayya da kasashen duniya,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Wakazalika, Shugaba na NAHCON ya bukaci kwamitin ya mayar da hankali wajen gudanar da ayyukan da aka ba shi, yana mai nanata musu cewa, aikin nasu na da matukar muhimmanci; don haka dole su mayar da hankali wajen yin abubuwan da suka dace, domin kyautata lamuran da suka shafi abincin alhazai da kuma masaukinsu a hajjin 2024 da ke tafe.

Yayin da yake nuna kwarin guiwarsa na cewa, kwamitin gabatar da shawarwari masu nagarta wadanda za a amfana da su, Arabi ya shaida cewa, kwamitin na da damar fadada ayyukansu ta yadda za su kawo shawarwari masu alfanu da ma’ana.

Idan ba a manta ba, a shekarar 2023 yayin gudanar da aikin hajji a kasa mai tsarki, Alhazan Nijeriya sun yi ta faman korafin matsalar masauki da ba su abinci mara inganci, wanda suka danganta hakan da kamfanin da aka dora wa alhakin ba su abincin da samar musu da masaukai.

NAHCON
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Ba Za A Cimma Wannan Yarjejeniya Ba Tare Da Taimakon Sin Ba

Ba Za A Cimma Wannan Yarjejeniya Ba Tare Da Taimakon Sin Ba

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.