• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin 2025: Gwamantin Tarayya Ta Zabi Kamfanonin Jirage 4 Don Jigilar Maniyyata

by Khalid Idris Doya
10 months ago
Hajjin

Gwamantin tarayya ta zakulo kamfanonin jiragen sama guda hudu da za ta yi amfani da su wajen jigilar maniyyatan Nijeriya zuwa kasar Saudiyya Arabiyya domin gudanar da aikin hajjin 2025. 

Shugaban hukumar kula da jin dadin alhazai na kasa (NAHCON), Abdullahi Usman, shi ne ya shaida hakan ta cikin sanarwar da jami’ar watsa labarai na hukumar, Fatima Usara, ta fitar a ranar Lahadi.

  • Kotu Ta Ɗaure Wasu Mutane 4 Da Ake Zargi Da Satar Birkin Jirgin Sama Guda 80 A Kano
  • Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai

Kamfanonin jiragen guda hudu da Nijeriya ta zaba a cewa sanarwar sun hada da Air Peace Limited, Fly-Nas, Mad Air, da kuma UMZA.

Wannan na zuwa ne bayan hukumar ta shirya jerin matakan yin zabin a watan Nuwamban 2024 da nufin zabo nagartattu kuma wadanda suka dace, inda kamfanonin jiragen 11 suka cika bukatar neman a ba su damar yin jigilar.

Idan za a tuna dai hukumar ta kafa kwamitin mutum 32 da za su bi jerin kamfanonin jirage 11 da suka cika bukatar neman kwangilar jigilar da nufin yin zabin da ya kamata domin kyautata harkokin jigilar.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Mambobin da suka hadu a kwamitin tantance da zaben jiragen saman sun hada da wakilai daga hukumomin jin dadin alhazai na jihohi, mambobi uku daga hukumar kula da sararin samaniyan Nijeriya (NCAA) da kuma mamba guda daga hukumar kula da jiragen sama ta Nijeriya (FAAN), hukumar kula da lafiyar sararin samaniya (NAMA), hukumar kula da yanayi ta kasa (NIMET), da kuma hukumar NSIB.

Kazalika, an zabi mamba daya daga hukumar kwastam, da hukumar yaki da cin hanci da rashawa (ICPC), an kuma dauki mambobi guda daga kowace shiyya a cikin mambobin majalisar NAHCON, shugabannin da suke kula da bangaren sufuri, Kasafi, harkokin shari’a, binciken kudi, ayyukan musamman dukka na NAHCON a matsayin mambobi a cikin kwamitin da kuma mamba daga masana’antar sufurin jirgin sama.

Bugu da kari, an zabi kamfanoni uku da za su yi jigilar kayayyaki yayin aikin hajjin da ke tafe. Wadanda suka samu tsallake tantance su ne, Aglow Abiation Support Serbices Limited, Cargozeal Technology Limited da kuma Kualla Inbestment Limited.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Da Yiwuwar Wasu Gwamnoni 5 Su Sauya Sheka Kafin Zaben 2027

Da Yiwuwar Wasu Gwamnoni 5 Su Sauya Sheka Kafin Zaben 2027

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.