• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin 2025: Gwamantin Tarayya Ta Zabi Kamfanonin Jirage 4 Don Jigilar Maniyyata

by Khalid Idris Doya
7 months ago
in Labarai
0
Hajjin 2025: Gwamantin Tarayya Ta Zabi Kamfanonin Jirage 4 Don Jigilar Maniyyata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamantin tarayya ta zakulo kamfanonin jiragen sama guda hudu da za ta yi amfani da su wajen jigilar maniyyatan Nijeriya zuwa kasar Saudiyya Arabiyya domin gudanar da aikin hajjin 2025. 

Shugaban hukumar kula da jin dadin alhazai na kasa (NAHCON), Abdullahi Usman, shi ne ya shaida hakan ta cikin sanarwar da jami’ar watsa labarai na hukumar, Fatima Usara, ta fitar a ranar Lahadi.

  • Kotu Ta Ɗaure Wasu Mutane 4 Da Ake Zargi Da Satar Birkin Jirgin Sama Guda 80 A Kano
  • Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai

Kamfanonin jiragen guda hudu da Nijeriya ta zaba a cewa sanarwar sun hada da Air Peace Limited, Fly-Nas, Mad Air, da kuma UMZA.

Wannan na zuwa ne bayan hukumar ta shirya jerin matakan yin zabin a watan Nuwamban 2024 da nufin zabo nagartattu kuma wadanda suka dace, inda kamfanonin jiragen 11 suka cika bukatar neman a ba su damar yin jigilar.

Idan za a tuna dai hukumar ta kafa kwamitin mutum 32 da za su bi jerin kamfanonin jirage 11 da suka cika bukatar neman kwangilar jigilar da nufin yin zabin da ya kamata domin kyautata harkokin jigilar.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Mambobin da suka hadu a kwamitin tantance da zaben jiragen saman sun hada da wakilai daga hukumomin jin dadin alhazai na jihohi, mambobi uku daga hukumar kula da sararin samaniyan Nijeriya (NCAA) da kuma mamba guda daga hukumar kula da jiragen sama ta Nijeriya (FAAN), hukumar kula da lafiyar sararin samaniya (NAMA), hukumar kula da yanayi ta kasa (NIMET), da kuma hukumar NSIB.

Kazalika, an zabi mamba daya daga hukumar kwastam, da hukumar yaki da cin hanci da rashawa (ICPC), an kuma dauki mambobi guda daga kowace shiyya a cikin mambobin majalisar NAHCON, shugabannin da suke kula da bangaren sufuri, Kasafi, harkokin shari’a, binciken kudi, ayyukan musamman dukka na NAHCON a matsayin mambobi a cikin kwamitin da kuma mamba daga masana’antar sufurin jirgin sama.

Bugu da kari, an zabi kamfanoni uku da za su yi jigilar kayayyaki yayin aikin hajjin da ke tafe. Wadanda suka samu tsallake tantance su ne, Aglow Abiation Support Serbices Limited, Cargozeal Technology Limited da kuma Kualla Inbestment Limited.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hajjin 2025Jirage
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Da Yiwuwar Wasu Gwamnoni 5 Su Sauya Sheka Kafin Zaben 2027

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

7 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

8 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

11 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

13 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

16 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

17 hours ago
Next Post
Da Yiwuwar Wasu Gwamnoni 5 Su Sauya Sheka Kafin Zaben 2027

Da Yiwuwar Wasu Gwamnoni 5 Su Sauya Sheka Kafin Zaben 2027

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.