• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Yiwuwar Wasu Gwamnoni 5 Su Sauya Sheka Kafin Zaben 2027

by Yusuf Shuaibu
6 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Da Yiwuwar Wasu Gwamnoni 5 Su Sauya Sheka Kafin Zaben 2027
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da zaben shekarar 2027 ke kara kunno kai, akwai zargi mai karfi na sauya sheka a tsakanin gwamnonin adawa guda 5 kafin zaben 2027, kamar yadda binciken LEADERSHIP ya tabbatar.

Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa gwamnonin Abiya, Aled Otti, da na Inugu, Peter Mbah da na Delta, Sheriff Oborebwori da na Ribas, Siminalayi Fubara da na Akwa Ibom, Umoh Eno, sun tattaunawa kan shirinsu na yin watsi da jam’iyyunsu tare da sauya sheka zuwa APC mai mulki.

  • Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai
  • Hamas Ta Amince Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Da Isra’ila

Yayin da Mbah, Fubara, Eno, Oborebwori na cikin babbar jam’iyyar adawa ta PDP, Otti na jam’iyyar LP ne. Dukkanin jam’iyyun biyu a fama da rikice-rikicen cikin gida bayan kammala zaben 2023.

Wasu majiyoyi sun shaida wa LEADERSHIP cewa, wasu daga cikin gwamnonin ana masu matsinlamba don su koma jam’iyyar APC mai mulki, wasu kuma na ganin cewa, bisa la’akari da rashin zaman lafiya a cikin jam’iyyarsu, a shirye suke su shiga wani jam’iyya da zai kara musu damar samun wa’adi na biyu.

Tun bayan dawowar mulkin dimokuradiyya a Nijeriya a shekarar 1999, gwamnoni sama da 20 ne suka bar jam’iyyunsu na siyasa. Jihohin da suka fi yawan gwamnonin da suka sauya sheka sun hada da Sakkwato, Imo, Abiya da Adamawa.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

A Sakkwato, gwamnoni uku suka sauya sheka a jam’iyyunsu na asali, yayin da gwamnoni biyu masu ci a Imo da Abiya da Zamfara da Adamawa suka sauya sheka.

Sai dai kuma maganar ficewa daga jam’iyyar gwamnan Abiya ya kara ta’azzara ne yayin kaddamar da ginin filin jirgin saman Abiya, ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ya bayyana cewa gwamnan Abiya zai koma APC.

Haka kuma, mataimakin shugaban majalisar wakilai, Benjamin Kalu, ya matsa wa Otti lamba ya koma APC.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa kawo yanzu ‘yan majalisar wakilai na jam’iyyar LP sama da 5 ne suka koma jam’iyyar APC.

A Jihar Ribas, Gwamna Fubara ya yi amfani da jam’iyyar APP wajen zaben kananan hukumomi, biyo bayan gazawar da ya yi wajen kwace tsarin PDP daga hannun Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ci gaba da tattaunawa cewa zai iya ficewa daga PDP kafin zaben 2027.

Kusancin gwamnan Jihar Akwa Ibom, Eno da shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio, kasancewarsa daya daga cikin jiga-jigan jam’iyyar APC na kasa, ya iya yin tasiri wajen janwo ra’ayin gwamnan zuwa jam’iyya mai mulki.

A Inugu, rikicin cikin gida da ke kawo cikas a cikin jam’iyyar PDP a matakin kasa na iya sa gwamnan ya karkatar da hankalinsa zuwa wata jam’iyya.

Shugabannin jam’iyyar PDP na Jihar Delta, karkashin jagorancin kungiyar shugabannin PDP, sun tofa albarkacin bakinsu game da soyayyar Oborebwori da shugabannin APC. Shugabannin jam’iyyar, wato Mista Theophilus Ekiyor, Mista Ochuko Oghenekome, da Mista Ezekiel Chukwudi, a wata budaddiyar wasika, sun zargi gwamnan da yin alaka a sirrance da shugaban ma’aikatan fadar gwamnati na Shugaban Kasa, Bola Tinubu, Hon. Femi Gbajabiamila da gwamnan Jihar Legas, Mista Babajide Sanwo-Olu, domin ya samu wa’adi na biyu a matsayin gwamnan Delta.

Shugabannin jam’iyyar PDP na Jihar Delta, sun tofa albarkacin bakinsu game da soyayyar Oborebwori da shugabannin APC. Shugabannin jam’iyyar, wato Mista Theophilus Ekiyor, Mista Ochuko Oghenekome, da Mista Ezekiel Chukwudi, a wata budaddiyar wasika, sun zargi gwamnan da yin akala a sirrance da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Hon. Femi Gbajabiamila da gwamnan Jihar Legas, Mista Babajide Sanwo-Olu, domin ya samu na wa’adi na biyu a matsayin gwamnan Delta.

Idan za a iya tunawa dai, dan majalisar tarayya kuma diyar tsohon gwamnan Jihar Delta, James Ibori, Hon. Erhiatake Ibori-Suenu, ta fice daga PDP zuwa APC a bara. Ibori dai ya yi zamani da Tinubu a matsayin gwamna a 1999 kuma makusancinsa ne.

Sai dai gwamnonin sun musanta wannan jita-jita, inda suka yi magana ta bakin mukarrabansu cewa ba za su bar jam’iyyarsu zuwa jam’iyyar APC mai mulki ba.

Haka zalika jam’iyyunsu sun bayyana irin wadannan ikirari a matsayin yaudarar jam’iyya mai mulki, inda suke neman haifar da rudani a cikin jam’iyyunsu da kuma zargin gwamnonin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2027GwamnoniZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hajjin 2025: Gwamantin Tarayya Ta Zabi Kamfanonin Jirage 4 Don Jigilar Maniyyata

Next Post

Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kaduna-Kano Cikin Watanni 14 – Gwamnati

Related

Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

6 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

6 days ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

6 days ago
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

4 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

4 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

1 month ago
Next Post
Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kaduna-Kano Cikin Watanni 14 – Gwamnati

Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kaduna-Kano Cikin Watanni 14 – Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.