• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Badi: Dalilin Kara Kudin Kujera Zuwa Naira Miliyan 4.5 – NAHCON

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Hajjin Badi

Hukumar Kula Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta umarci hukumomin aikin hajji na jihohi su fara amsar naira miliyan 4.5 daga hannun maniyyata a matsayin kudin ajiyar aikin hajjin badi, 2024.

Da yake bayani bayan kammala taro da sakatarorin hukumomin aikin hajji na ji-hohi a hedikwatar hukumar da ke Abuja, shugaban hukumar NAHCON, Zikrullah Hassan ya ce kudin tafiya aikin hajji na shekara mai zuwa zai kasance da tsada sakamakon daidaita farashin dala da gwamnatin tarayya ta yi, sai dai kuma ya kara jaddada cewa kudin ajiyar na iya canzawa wannan kuma ya danganta ne kan yadda darajar naira ta kasance nan gaba.

  • Sakon Shugaban Kasar Sin Ya Nuna Makomar Aikin Raya Tattalin Arziki Mai Alaka Da Fasahohin Zamani
  • Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Jam’iyyar APM Ta Shigar Kan Ingancin Shettima

Maniyyata aikin hajji na shekarar 2023 sun biya naira miliyan 2.8, hakan ta kasance ne saboda a lokacin ana sayar da kowacce dala daya kan naira 450.

Ya ce, “Kamar yadda muke magana a yanzu, ana sayar da kowacce dalar Amurka daya kan naira 740. Don haka idan ka lissafa kan yadda aka sayar da dala a hajjin bara, yi tunanin miliyoyin da kake bukata a kudin aikin hajji a shekarar 2024. Lallai a yi shiri sosai domin kudin aikin hajjin 2024 zai yi tsada,” in ji shi.

Ya kara da cewa idan har farashin canji ya ragu, farashin kudin aikin hajjin zai ra-gu, idan kuma farashin canjin kudi ya karu, to dole ne kudin aikin hajji ya karu.

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

Shugaban hukumar NAHCON ya sanar da cewa Masarautar Saudiyya ta fitar da kalandar aikin hajjin 2024, inda ya kara da cewa nan da ranar 29 ga watan Afrilun shekarar 2024 za a rufe bayar da bizar aikin hajji, yayin da ya rage kwana 10 alhazai su fara isa kasa mai tsarki domin gudanar da ibada.

Ya kara da cewa, sabanin yadda ake yi a baya, zuwa aikin hajji na gaba, ma-hukuntan Saudiyya na son sanin adadin maniyyatan da ke zuwa daga kowace kasa kwana 40 zuwa 50 kafin Arafat.

Da ya dauko batun ayyukan hajjin 2023, Hassan ya sanar da cewa hukumar ta samu nasarori duk da wasu kalubale da ta fuskanta.

A cewarsa, a karon farko tun shekarar 2013, hukumar ta samu damar jigilar duk-kan alhazan Nijeriya sama da 90,000 da suka yi rajista kuma aka ba su biza.

Ya sanar da cewa an shafe kwanaki 28 don jigilar alhazai zuwa Saudiyya, yayin da aka kwashe kwanaki ana dawo da su daga kasar.

Da yake magana kan kalubalen da mahajjata suka samu a garin Muna, ya ce NA-HCON ta kafa kwamiti tun kafin kammala aikin hajjin 2023, tare da rubuta wa hukumomin Saudiyya wasikar mayar musu da kudaden da suka biya, sannan ku-ma ta nemi gafarar mahajjatan Nijeriya.

“Hajjin 2023 ya zo ya wuce kuma mun samu nasara kan yadda muka samu damar daukar dukkan alhazan da aka ba su biza zuwa kasar Saudiyya.

“2023 ita ce shekarar da za mu iya kai wannan adadi mai yawa zuwa Saudiyya bayan 2013, shekaru 10 da suka gabata. A bana an kai alhazan Nijeriya 95,000 zuwa kasar Saudiyya lafiya.

“Na biyu shi ne, mun rasa wasu alhazai. Allah ya gafarta musu zunubansu ya shi-gar da su Aljannah. Adadin alhazan da muka rasa ba su da yawa, amma muna fa-tan zai ragu.

“Muna kuma sane da cewa akwai kalubale a Muna, musamman saboda wuraren da aka bai wa ‘yan Nijeriya ba su isa ba, sannan an samu karancin abinci.

“An kafa wani kwamiti da zai duba wadannan kura-kuran kuma kafin mu bar Saudiyya mun nemi a mayar mana da kudaden da muka bayar tare da neman gafara.

“Yayin da muke jiran maido da martani, ina so in sanar da ku a wannan matakin cewa an fara shirye-shiryen Hajj 2024,” in ji Hassan.

Jaridar Tribune ta ruwaito cewa alhazan Nijeriya da suka je Saudiyya aikin hajjin 2023 sun biya tsakanin naira miliyan 2.88 zuwa naira miliyan 2.99.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya
Manyan Labarai

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Manyan Labarai

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 
Manyan Labarai

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Next Post
NIS Reshen Jihar Ribas Ta Nada Queen Stephanie Jakadiyar Fasfo

NIS Reshen Jihar Ribas Ta Nada Queen Stephanie Jakadiyar Fasfo

LABARAI MASU NASABA

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.