ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Badi: Dalilin Kara Kudin Kujera Zuwa Naira Miliyan 4.5 – NAHCON

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Hajjin Badi

Hukumar Kula Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta umarci hukumomin aikin hajji na jihohi su fara amsar naira miliyan 4.5 daga hannun maniyyata a matsayin kudin ajiyar aikin hajjin badi, 2024.

Da yake bayani bayan kammala taro da sakatarorin hukumomin aikin hajji na ji-hohi a hedikwatar hukumar da ke Abuja, shugaban hukumar NAHCON, Zikrullah Hassan ya ce kudin tafiya aikin hajji na shekara mai zuwa zai kasance da tsada sakamakon daidaita farashin dala da gwamnatin tarayya ta yi, sai dai kuma ya kara jaddada cewa kudin ajiyar na iya canzawa wannan kuma ya danganta ne kan yadda darajar naira ta kasance nan gaba.

  • Sakon Shugaban Kasar Sin Ya Nuna Makomar Aikin Raya Tattalin Arziki Mai Alaka Da Fasahohin Zamani
  • Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Jam’iyyar APM Ta Shigar Kan Ingancin Shettima

Maniyyata aikin hajji na shekarar 2023 sun biya naira miliyan 2.8, hakan ta kasance ne saboda a lokacin ana sayar da kowacce dala daya kan naira 450.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Kamar yadda muke magana a yanzu, ana sayar da kowacce dalar Amurka daya kan naira 740. Don haka idan ka lissafa kan yadda aka sayar da dala a hajjin bara, yi tunanin miliyoyin da kake bukata a kudin aikin hajji a shekarar 2024. Lallai a yi shiri sosai domin kudin aikin hajjin 2024 zai yi tsada,” in ji shi.

Ya kara da cewa idan har farashin canji ya ragu, farashin kudin aikin hajjin zai ra-gu, idan kuma farashin canjin kudi ya karu, to dole ne kudin aikin hajji ya karu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Shugaban hukumar NAHCON ya sanar da cewa Masarautar Saudiyya ta fitar da kalandar aikin hajjin 2024, inda ya kara da cewa nan da ranar 29 ga watan Afrilun shekarar 2024 za a rufe bayar da bizar aikin hajji, yayin da ya rage kwana 10 alhazai su fara isa kasa mai tsarki domin gudanar da ibada.

Ya kara da cewa, sabanin yadda ake yi a baya, zuwa aikin hajji na gaba, ma-hukuntan Saudiyya na son sanin adadin maniyyatan da ke zuwa daga kowace kasa kwana 40 zuwa 50 kafin Arafat.

Da ya dauko batun ayyukan hajjin 2023, Hassan ya sanar da cewa hukumar ta samu nasarori duk da wasu kalubale da ta fuskanta.

A cewarsa, a karon farko tun shekarar 2013, hukumar ta samu damar jigilar duk-kan alhazan Nijeriya sama da 90,000 da suka yi rajista kuma aka ba su biza.

Ya sanar da cewa an shafe kwanaki 28 don jigilar alhazai zuwa Saudiyya, yayin da aka kwashe kwanaki ana dawo da su daga kasar.

Da yake magana kan kalubalen da mahajjata suka samu a garin Muna, ya ce NA-HCON ta kafa kwamiti tun kafin kammala aikin hajjin 2023, tare da rubuta wa hukumomin Saudiyya wasikar mayar musu da kudaden da suka biya, sannan ku-ma ta nemi gafarar mahajjatan Nijeriya.

“Hajjin 2023 ya zo ya wuce kuma mun samu nasara kan yadda muka samu damar daukar dukkan alhazan da aka ba su biza zuwa kasar Saudiyya.

“2023 ita ce shekarar da za mu iya kai wannan adadi mai yawa zuwa Saudiyya bayan 2013, shekaru 10 da suka gabata. A bana an kai alhazan Nijeriya 95,000 zuwa kasar Saudiyya lafiya.

“Na biyu shi ne, mun rasa wasu alhazai. Allah ya gafarta musu zunubansu ya shi-gar da su Aljannah. Adadin alhazan da muka rasa ba su da yawa, amma muna fa-tan zai ragu.

“Muna kuma sane da cewa akwai kalubale a Muna, musamman saboda wuraren da aka bai wa ‘yan Nijeriya ba su isa ba, sannan an samu karancin abinci.

“An kafa wani kwamiti da zai duba wadannan kura-kuran kuma kafin mu bar Saudiyya mun nemi a mayar mana da kudaden da muka bayar tare da neman gafara.

“Yayin da muke jiran maido da martani, ina so in sanar da ku a wannan matakin cewa an fara shirye-shiryen Hajj 2024,” in ji Hassan.

Jaridar Tribune ta ruwaito cewa alhazan Nijeriya da suka je Saudiyya aikin hajjin 2023 sun biya tsakanin naira miliyan 2.88 zuwa naira miliyan 2.99.

Hajjin Badi
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
NIS Reshen Jihar Ribas Ta Nada Queen Stephanie Jakadiyar Fasfo

NIS Reshen Jihar Ribas Ta Nada Queen Stephanie Jakadiyar Fasfo

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.