• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Badi: Dalilin Kara Kudin Kujera Zuwa Naira Miliyan 4.5 – NAHCON

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Labarai, Manyan Labarai
0
Hajjin Badi: Dalilin Kara Kudin Kujera Zuwa Naira Miliyan 4.5 – NAHCON
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta umarci hukumomin aikin hajji na jihohi su fara amsar naira miliyan 4.5 daga hannun maniyyata a matsayin kudin ajiyar aikin hajjin badi, 2024.

Da yake bayani bayan kammala taro da sakatarorin hukumomin aikin hajji na ji-hohi a hedikwatar hukumar da ke Abuja, shugaban hukumar NAHCON, Zikrullah Hassan ya ce kudin tafiya aikin hajji na shekara mai zuwa zai kasance da tsada sakamakon daidaita farashin dala da gwamnatin tarayya ta yi, sai dai kuma ya kara jaddada cewa kudin ajiyar na iya canzawa wannan kuma ya danganta ne kan yadda darajar naira ta kasance nan gaba.

  • Sakon Shugaban Kasar Sin Ya Nuna Makomar Aikin Raya Tattalin Arziki Mai Alaka Da Fasahohin Zamani
  • Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Jam’iyyar APM Ta Shigar Kan Ingancin Shettima

Maniyyata aikin hajji na shekarar 2023 sun biya naira miliyan 2.8, hakan ta kasance ne saboda a lokacin ana sayar da kowacce dala daya kan naira 450.

Ya ce, “Kamar yadda muke magana a yanzu, ana sayar da kowacce dalar Amurka daya kan naira 740. Don haka idan ka lissafa kan yadda aka sayar da dala a hajjin bara, yi tunanin miliyoyin da kake bukata a kudin aikin hajji a shekarar 2024. Lallai a yi shiri sosai domin kudin aikin hajjin 2024 zai yi tsada,” in ji shi.

Ya kara da cewa idan har farashin canji ya ragu, farashin kudin aikin hajjin zai ra-gu, idan kuma farashin canjin kudi ya karu, to dole ne kudin aikin hajji ya karu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Shugaban hukumar NAHCON ya sanar da cewa Masarautar Saudiyya ta fitar da kalandar aikin hajjin 2024, inda ya kara da cewa nan da ranar 29 ga watan Afrilun shekarar 2024 za a rufe bayar da bizar aikin hajji, yayin da ya rage kwana 10 alhazai su fara isa kasa mai tsarki domin gudanar da ibada.

Ya kara da cewa, sabanin yadda ake yi a baya, zuwa aikin hajji na gaba, ma-hukuntan Saudiyya na son sanin adadin maniyyatan da ke zuwa daga kowace kasa kwana 40 zuwa 50 kafin Arafat.

Da ya dauko batun ayyukan hajjin 2023, Hassan ya sanar da cewa hukumar ta samu nasarori duk da wasu kalubale da ta fuskanta.

A cewarsa, a karon farko tun shekarar 2013, hukumar ta samu damar jigilar duk-kan alhazan Nijeriya sama da 90,000 da suka yi rajista kuma aka ba su biza.

Ya sanar da cewa an shafe kwanaki 28 don jigilar alhazai zuwa Saudiyya, yayin da aka kwashe kwanaki ana dawo da su daga kasar.

Da yake magana kan kalubalen da mahajjata suka samu a garin Muna, ya ce NA-HCON ta kafa kwamiti tun kafin kammala aikin hajjin 2023, tare da rubuta wa hukumomin Saudiyya wasikar mayar musu da kudaden da suka biya, sannan ku-ma ta nemi gafarar mahajjatan Nijeriya.

“Hajjin 2023 ya zo ya wuce kuma mun samu nasara kan yadda muka samu damar daukar dukkan alhazan da aka ba su biza zuwa kasar Saudiyya.

“2023 ita ce shekarar da za mu iya kai wannan adadi mai yawa zuwa Saudiyya bayan 2013, shekaru 10 da suka gabata. A bana an kai alhazan Nijeriya 95,000 zuwa kasar Saudiyya lafiya.

“Na biyu shi ne, mun rasa wasu alhazai. Allah ya gafarta musu zunubansu ya shi-gar da su Aljannah. Adadin alhazan da muka rasa ba su da yawa, amma muna fa-tan zai ragu.

“Muna kuma sane da cewa akwai kalubale a Muna, musamman saboda wuraren da aka bai wa ‘yan Nijeriya ba su isa ba, sannan an samu karancin abinci.

“An kafa wani kwamiti da zai duba wadannan kura-kuran kuma kafin mu bar Saudiyya mun nemi a mayar mana da kudaden da muka bayar tare da neman gafara.

“Yayin da muke jiran maido da martani, ina so in sanar da ku a wannan matakin cewa an fara shirye-shiryen Hajj 2024,” in ji Hassan.

Jaridar Tribune ta ruwaito cewa alhazan Nijeriya da suka je Saudiyya aikin hajjin 2023 sun biya tsakanin naira miliyan 2.88 zuwa naira miliyan 2.99.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumomin Sin Sun Fitar Da Wasu Ka’idoji Don Inganta Tsaron Wuraren Hakar Ma’adinai

Next Post

NIS Reshen Jihar Ribas Ta Nada Queen Stephanie Jakadiyar Fasfo

Related

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
Labarai

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

1 hour ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

2 hours ago
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

9 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

9 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

12 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

13 hours ago
Next Post
NIS Reshen Jihar Ribas Ta Nada Queen Stephanie Jakadiyar Fasfo

NIS Reshen Jihar Ribas Ta Nada Queen Stephanie Jakadiyar Fasfo

LABARAI MASU NASABA

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.