ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Badi: Dalilin Kara Kudin Kujera Zuwa Naira Miliyan 4.5 – NAHCON

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Hajjin Badi

Hukumar Kula Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta umarci hukumomin aikin hajji na jihohi su fara amsar naira miliyan 4.5 daga hannun maniyyata a matsayin kudin ajiyar aikin hajjin badi, 2024.

Da yake bayani bayan kammala taro da sakatarorin hukumomin aikin hajji na ji-hohi a hedikwatar hukumar da ke Abuja, shugaban hukumar NAHCON, Zikrullah Hassan ya ce kudin tafiya aikin hajji na shekara mai zuwa zai kasance da tsada sakamakon daidaita farashin dala da gwamnatin tarayya ta yi, sai dai kuma ya kara jaddada cewa kudin ajiyar na iya canzawa wannan kuma ya danganta ne kan yadda darajar naira ta kasance nan gaba.

  • Sakon Shugaban Kasar Sin Ya Nuna Makomar Aikin Raya Tattalin Arziki Mai Alaka Da Fasahohin Zamani
  • Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Jam’iyyar APM Ta Shigar Kan Ingancin Shettima

Maniyyata aikin hajji na shekarar 2023 sun biya naira miliyan 2.8, hakan ta kasance ne saboda a lokacin ana sayar da kowacce dala daya kan naira 450.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Kamar yadda muke magana a yanzu, ana sayar da kowacce dalar Amurka daya kan naira 740. Don haka idan ka lissafa kan yadda aka sayar da dala a hajjin bara, yi tunanin miliyoyin da kake bukata a kudin aikin hajji a shekarar 2024. Lallai a yi shiri sosai domin kudin aikin hajjin 2024 zai yi tsada,” in ji shi.

Ya kara da cewa idan har farashin canji ya ragu, farashin kudin aikin hajjin zai ra-gu, idan kuma farashin canjin kudi ya karu, to dole ne kudin aikin hajji ya karu.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Shugaban hukumar NAHCON ya sanar da cewa Masarautar Saudiyya ta fitar da kalandar aikin hajjin 2024, inda ya kara da cewa nan da ranar 29 ga watan Afrilun shekarar 2024 za a rufe bayar da bizar aikin hajji, yayin da ya rage kwana 10 alhazai su fara isa kasa mai tsarki domin gudanar da ibada.

Ya kara da cewa, sabanin yadda ake yi a baya, zuwa aikin hajji na gaba, ma-hukuntan Saudiyya na son sanin adadin maniyyatan da ke zuwa daga kowace kasa kwana 40 zuwa 50 kafin Arafat.

Da ya dauko batun ayyukan hajjin 2023, Hassan ya sanar da cewa hukumar ta samu nasarori duk da wasu kalubale da ta fuskanta.

A cewarsa, a karon farko tun shekarar 2013, hukumar ta samu damar jigilar duk-kan alhazan Nijeriya sama da 90,000 da suka yi rajista kuma aka ba su biza.

Ya sanar da cewa an shafe kwanaki 28 don jigilar alhazai zuwa Saudiyya, yayin da aka kwashe kwanaki ana dawo da su daga kasar.

Da yake magana kan kalubalen da mahajjata suka samu a garin Muna, ya ce NA-HCON ta kafa kwamiti tun kafin kammala aikin hajjin 2023, tare da rubuta wa hukumomin Saudiyya wasikar mayar musu da kudaden da suka biya, sannan ku-ma ta nemi gafarar mahajjatan Nijeriya.

“Hajjin 2023 ya zo ya wuce kuma mun samu nasara kan yadda muka samu damar daukar dukkan alhazan da aka ba su biza zuwa kasar Saudiyya.

“2023 ita ce shekarar da za mu iya kai wannan adadi mai yawa zuwa Saudiyya bayan 2013, shekaru 10 da suka gabata. A bana an kai alhazan Nijeriya 95,000 zuwa kasar Saudiyya lafiya.

“Na biyu shi ne, mun rasa wasu alhazai. Allah ya gafarta musu zunubansu ya shi-gar da su Aljannah. Adadin alhazan da muka rasa ba su da yawa, amma muna fa-tan zai ragu.

“Muna kuma sane da cewa akwai kalubale a Muna, musamman saboda wuraren da aka bai wa ‘yan Nijeriya ba su isa ba, sannan an samu karancin abinci.

“An kafa wani kwamiti da zai duba wadannan kura-kuran kuma kafin mu bar Saudiyya mun nemi a mayar mana da kudaden da muka bayar tare da neman gafara.

“Yayin da muke jiran maido da martani, ina so in sanar da ku a wannan matakin cewa an fara shirye-shiryen Hajj 2024,” in ji Hassan.

Jaridar Tribune ta ruwaito cewa alhazan Nijeriya da suka je Saudiyya aikin hajjin 2023 sun biya tsakanin naira miliyan 2.88 zuwa naira miliyan 2.99.

Hajjin Badi
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
NIS Reshen Jihar Ribas Ta Nada Queen Stephanie Jakadiyar Fasfo

NIS Reshen Jihar Ribas Ta Nada Queen Stephanie Jakadiyar Fasfo

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.