• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Hajjin Bana

Hukumar jin dadin alhazai ta kasa (NAHCON) ta ce bayar da biza 73,310 daga cikin kujeru 75,000 da aka ware wa jihohi domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2023.

Da yake jawabi yayin ganawa da manema labarai ranar Talata a Abuja, Shugaban Hukumar NAHCON, Zikrullah Hassan ya bayyana cewa hukumar ta kwashe maniyyata 46,258 zuwa kasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin bana tun daga ranar 25 ga watan Mayu da aka fara jigilar maniyyata.

  • Kungiya Ta Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Inganta Tsaro Da Yaki Da Rashawa
  • Hikimar Kasar Sin Ta Ba Da Gudummuwa Ga Ci Gaban Kungiyar SCO

Shugaban hukumar wanda ya samu wakilcin Kwamishinan NAHCON na bangaren tsare-tsare, Bincike, kididdiga, watsa labarai da ayyukan dakin karatu, Sheikh Suleiman Momoh ya bayyana cewa duk da wasu kalubale da ake fuskanta a lokacin aikin jigilar maniyyata, hukumar ba za ta bar kowa daga cikin maniyyatan da suka yi rajista ba.

“Akwai wasu kalubale da muke fuskanta saboda lalacewar na’urorin, amma muna himma don tabbatar da cewa duk wani yanayi da ya faru za mu dauki matakin gaggawa wajen shawo kan lamarin tare da mayar da abubuwa yadda suke.”

Ya kara da cewa, an tanadi masauki da ciyarwa da mahajjata mai kyau a Madina, yayin da hukumar ke tabbatar da cewa dukkan majiyyata sun gudanar da ibadarsu yadda ya dace a can.

LABARAI MASU NASABA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Ya kuma bayyana cewa a karon farko kasar ta cika dukkan rarar da aka bai wa hukumar sakamakon koma-bayan da maniyyatan suka samu lokacin cutar Karona.

Ya ce yayin da ya rage na makwanni biyu a fara aikin hajji, hukumar za ta tabbatar da cewa dukkan maniyyatan suna kasar Saudiyya kafin lokaci ya kure.

“Muna duban wuraren da aka samu nasara da kuma wanda aka samu nakasu, amma muna tabbatar da cewa babu wani maniyyaci da ya yi rajista da ba za a kai shi kasa mai tsarki ba kafin wa’adi ya kare,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza
Labarai

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
Labarai

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya

November 8, 2025
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

An Cafke Matashi Yana Tsaka Da Yi Wa ‘Yar Shekara 2 Fyade

LABARAI MASU NASABA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.