• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiya Ta Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Inganta Tsaro Da Yaki Da Rashawa

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Kungiya Ta Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Inganta Tsaro Da Yaki Da Rashawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Arewa New Agenda, mai fafutukar kare martaba da shigar Arewa cikin harkokin kasa, ta yaba wa Shugaban Kasa Ahmed Bola Tinubu bisa tsarin shugabancinsa tun hawansa mulki makonni biyu da suka gabata.

Shugaban kungiyar Sanata Ahmed Abubakar MoAllahyidi ne ya yi wannan yabon a wata ganawa da manema labarai a Abuja ranar Juma’a.

Arewa New Agenda ta bayyana wasu muhimman shawarwari da matakan da shugaban kasan ya dauka tun bayan hawansa mulki, wadanda suka hada da: soke tallafin man fetur, hana yajin aikin da kungiyoyin kwadago suka shirya yi a fadin kasa, da kafa tsarin kudin musaya na Naira bai-daya, da ganawa da shuwagabannin hukumomi masu muhimmanci tare da kai ziyara a cibiyoyin tsaro da tattara bayanan sirri da sauransu.

A cewar MoAllahyidi, “Wadannan matakai sun nuna jajircewar Shugaba Tinubu wajen tunkarar muhimman al’amurra a kasar nan da kuma samar da jagoranci nagari a harkokin mulki”.

“Nade-naden da Shugaba Tinubu ya yi ya haifar da samun kwarin gwiwa a kan ingantuwar tsaro da kuma yaki da cin hanci da rashawa”.

Labarai Masu Nasaba

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

“Muna farin ciki da cewa shugaban kasa Tinubu, wanda kungiyar ta goyi bayansa a lokacin da yake neman takararsa a jam’iyyar APC kuma ya lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2023, ya fara aikinsa da kafar dama.”

tinubu

“Shugaba Tinubu ya yanke shawarar nada masu ba da shawara na musamman guda takwas, kuma wannan matakin ya samu karbuwa da farin ciki a fadin kasar nan, ciki har da ‘yan adawa. Wani abin lura a cikin wannan ci gaban shi ne babu wata adawa ko rashin jituwa dangane da wadannan nade-nade, wanda ke nuni da goyon bayan zaben da aka yi wa shugaban kasar.

“Wani nadin da ya sanya farin ciki a fadin kasar nan shi ne na mai ba da shawara na musamman kan harkokin tsaro. ‘Yan Nijeriya na da kyakkyawan fata na cewa Shugaba Tinubu zai magance kalubalen tsaro yadda ya kamata a wannan karon”.

A baya dai ANA ta jaddada cewa nasara ko gazawar da Tinubu zai samu zai ta’allaka ne a kan ayyukansa na yaki da rashin tsaro da cin hanci da rashawa, wadanda su ne manyan batutuwa biyu da suka addabi al’ummar kasar nan.

Daga cikin fitattun wadanda aka nada akwai Malam Nuhu Ribadu, wanda a baya ya rike mukamin Shugaban Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) a shekarar 2003. Idan aka duba, Ribadu, tarihinsa na nuna irin kishinsa, sadaukarwa, da kwazonsa na musamman wajen yaki da cin hanci da rashawa. A lokacin da yake rike da mukamin a hukumar ta EFCC, ya sa ido a kan kafa cibiyar horarwa a kan nazarin manyan laifuka da bincike, wanda hakan ya kara tabbatar da martabar hukumar a matsayin babbar hukumar tabbatar da doka a Afirka.

tinubu

Ribadu ya jajirce wajen neman adalci har aka karrama shi a matsayin wanda ake girmamawa a matsayin dan gwagwarmayar yaki da cin hanci da rashawa a duniya. Kin karbar cin hancin Naira miliyan 30 a shekarar 2005 da kuma cin hancin dala miliyan 15 daga hannun tsohon gwamna a 2007 a shekarar 2007 ya zama abin kwatance game da da’ar aiki.

Bugu da kari, Ribadu ya taka muhimmiyar rawa wajen fitar da Nijeriya daga cikin jerin kasashen kungiyar FATF, da samun damar shigarta kungiyar Egmont, da kuma tabbatar da janye Jami’an da ke sanya ido a kan manyan laifukan kudi a Baitul-malin Amurka daga Nijeriya.

A karshen taron dai, Arewa New Agenda ta yaba wa shugaban kasa Ahmed Bola Tinubu bisa kyakkawan jagorancinsa da tsarin gudanar da mulkinsa a cikin makonni biyun farko da hawansa karagai. Kungiyar ta yi imanin cewa, matakin da shugaban kasar ya dauka da abubuwan da yake aiwatarwa ne ya sanya Nijeriya ta fara jin kamshin kyakkyawar makoma.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: jagoranciKasaNijeriyaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hikimar Kasar Sin Ta Ba Da Gudummuwa Ga Ci Gaban Kungiyar SCO

Next Post

Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya

Related

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

13 hours ago
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

14 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

14 hours ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

15 hours ago
Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue
Labarai

Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

16 hours ago
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
Manyan Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

18 hours ago
Next Post
Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya

Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

July 4, 2025
Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.