• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hakika Maganar “Tarkon Bashi” Tarko Ne Na Tunani

by CMG Hausa
2 years ago
Variety of the African banknotes

Variety of the African banknotes

Wani abokina ya kan buga mana waya daga jihar Kano ta Najeriya don mu gaisa da juna, sai dai yawan waya da ya buga mun a wadannan kwanaki ya ragu. Daga baya na fahimci dalilin da ya sa haka, wato hauhawar farashin kaya ta sa shi fuskantar matsin lamba a fannin rayuwa, don haka ya fara tsimin kudin da yake kashewa a fannin sadarwa. Misalinsa ya nuna yadda ake fama da mawuyacin hali a kasar Najeriya, gami da kasashe daban daban na Afrika.

Wannan yanayi mai wuya a fannin tattalin arziki ya sa kasashen Afrika samun matsalar biyan bashin da ake binsu. Ganin haka ya sa wasu jami’an kasar Amurka sake fara kokarin haifar da matsala ga huldar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afrika, inda suka ce wai kasar Sin ta yi karan tsaye ga aikin yafewa kasashen Afrika basusukan da ake binsu. A bisa ra’ayin wasu mutane na kasar Amurka, da na wasu kasashen dake yammacin duniya, duk wani rancen da kasar Sin ta samar “tarkon bashi” ne, wanda ke da nufin lahanta moriyar kasashen Afrika.

  • Xi Jinping: Akwai Makoma Mai Haske A Fannin Raya Sana’o’i Na Musamman A Yankunan Karkara

Batun nan ya sa ni tunawa da wata tsohuwar maganar da mu Sinawa mu kan fada, wato “Idan ana neman dorawa wani laifi, to, ba za a rasa hujja ba.” Sai dai karya kome dadinta, ba gaskiya ba ce.

Mene ne gaskiyar lamarin?

Na farko, bashin da kasar Sin ta samar wani karamin bangare ne na daukacin basussukan da ake bin kasashen Afrika.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Wata kungiyar da ba ta gwamnati ba dake kasar Birtaniya mai suna Debt Justice ta sanar da wani rahoto a watan Yulin bara, wanda ya nuna cewa kashi 35% na basusukan da kasashen Afrika suke ci sun zo ne daga kamfanonin ba da rance masu zaman kansu dake kasashen yammacin duniya, inda adadin kudin rancen da suka samar wa kasashen Afrika ya ninka na kasar Sin har sau 3. Ban da wannan kuma, su manyan hukumomin hada-hadar kudi na kasa da kasa, irinsu bankin duniya, da hukumar ba da lamuni ta duniya, su ma sun samar da dimbin bashi ga kasashen Afrika, kana manyan ’yan kasuwa masu rike da mafi yawan hannayen jarin wadannan hukumomi suna kasar Amurka da kuma kasashen Turai.

Na biyu shi ne, kasar Sin na samar da bashi mai rangwamen kudin ruwa ga kasashen Afrika, gami da kokarin rage musu matsin lamba a fannin biyan bashi.

Bashin da kasar Sin ke samar wa kasashen Afrika, ruwansa ya yi kasa da ruwan bashin da sauran kasashe ke bayarwa wanda ya kan kai kashi 5%, kana Sin ba ta taba gindaya wani sharadi maras dacewa yayin da take ba da rance ba. Ban da haka, kasar Sin tana kokarin taka rawa a shawarar da kungiyar G20 ta bayar ta dakatar da biyan bashi, inda ta kulla yarjejeniya ko kuma cimma matsaya ta tsawaita wa’adin biyan bashi tare da kasashe 19 dake nahiyar Afrika. Cikin wani sabon rahoton nazari da jami’ar Johns Hopkins ta kasar Amurka ta gabatar, an ce yawan bashin da kasar Sin ta dakatar da lokacin biyansa ya kai kashi 63% cikin dukkan basusukan da mambobin kungiyar G20 suka tsawaita wa’adinsu.

Sa’an nan na 3 shi ne, ba kasar Sin ce ta sa kasashen Afrika fuskantar mawuyacin hali a fannin tattalin arziki, da kasa biyan bashin da ake binsu ba.

Yadda bankunan kasar Amurka suka kara yawan ruwan ajiyar kudi, da karuwar darajar dalar Amurka, suna janyo dimbin kudi zuwa kasuwannin kasar Amurka daga kasashe daban daban. Lamarin da ya sa kasashen Afrika karancin jarin da ake zuba musu, da rashin kudin musaya da ake bukata yayin da ake ciniki tsakanin kasa da kasa, kana kudin da suke kashewa wajen neman bashi a kasuwannin kasa da kasa ya karu sosai. Ban da haka, kasar Amurka na ta kokarin neman tsananta yanayin da ake ciki a yakin da ake yi tsakanin kasar Rasha da ta Ukraine, abun da ya haddasa daddadiyar hauhawar farashin abinci, da na sauran kayayyakin masarufi, ta yadda kasashen Afrika ke fuskantar matsin lamba sosai a fannin tattalin arziki. Wadannan dalilai da tasirin annobar cutar COVID-19, su ne suka jefa kasashen Afrika cikin wani mawuyacin hali.

Sai dai wasu mutane na kasar Amurka, da na wasu kasashen yammacin duniya, sun rufe ido a gabanin ainihin abun da ya faru, inda suka dinga ruta maganar “ tarkon bashi” na kasar Sin. Hakika suna neman sanya kasashen Afrika fadawa cikin tarko na tunani. Wannan “tarko” wata fasaha ce da mutanen kasashen yammacin duniya su kan yi amfani da ita a lokacin da suke muhawara da juna, wato “Poisoning the well” (zuba guba cikin rijiya). Idan an zuba guba cikin rijiya, ba za a iya shan ruwan da aka debo daga rijiyar ba. An yi amfani da kalmomin wajen siffanta yadda ake shafa wa wani mutum kashin kaza. Sa’an nan bayan da aka bata sunan mutum, to, ba za a sake amincewa da maganarsa ba. Abun da wasu mutane na kasar Amurka da na wasu kasashen yammacin duniya suke nema ke nan, wato bata sunan kasar Sin, don girgiza imanin da kasashen Afrika suke da shi kan kasar ta Sin, ta yadda za a lalata hulda mai kyau dake tsakanin kasashen Afrika da kasar Sin, da hana kasashe masu tasowa samun ci gaba. Kawai suna neman kare matsayin kasashen yamma na kan gaba a duniya, da ikonsu na ba da umarni ga saura, musamman ma a fannin kula da harkokin kasa da kasa.

Abokaina, a ganinku, za su cimma burinsu kuwa? (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Yadda Hadarin Mota Ya Raunata Mutane 14 A Hanyar Bauchi

Yadda Hadarin Mota Ya Raunata Mutane 14 A Hanyar Bauchi

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.