• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halin Rigakafin Annoba A Amurka Yana Da Ban Tsoro, Ta Yaya Za Ta Nuna Yatsa Ga Saura?

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Halin Rigakafin Annoba A Amurka Yana Da Ban Tsoro, Ta Yaya Za Ta Nuna Yatsa Ga Saura?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa kididdigar da Cibiyar Kula da Cututtuka ta Amurka ta fitar, kasar Amurka ta fuskanci bala’in annobar COVID-19 har sau biyar a cikin shekaru uku da suka gabata. Kuma a duk lokacin da adadin masu kamuwa da cutar ya kai matsayin koli, ana samun rahotanni masu yawa, game da yadda ake samun kusan rugujewar tsarin aikin likitancin kasar.

Sakamakon sakaci da aiki da gwamnatin Amurka ke yi, kusan dukkanin nau’ikan cutar COVID-19 sun taba yaduwa a kasar, wanda hakan ya haddasa harbuwar mutane sama da miliyan 100 a kasar, kana sama da mutane miliyan 1.08 sun mutu, baya ga yara 250,000 da suka zama marayu saboda kisan da annobar ta yi, inda matsanancin halin da kasar ke ciki ya sanya ta kan gaba a fannin fama da cutar a duniya.

  • Sin Ta Inganta Inshorar Likitanci Don Saukaka Kudaden Da Masu Fama Da Cutar COVID-19 Ke Kashewa

Wasu manazarta sun yi nuni da cewa, ainihin abin da ya haifar da yanayin da ake ciki shi ne, yadda gwamnatin Amurka ba ta taba sadaukar da karfinta ga aikin magance hakikanin matsalolin da take da fuskanta ba, maimakon hakan tana ta siyasantar da batun annobar.

Sabanin haka, kasar Sin ta aiwatar da matakai daban daban a cikin shekarun ukun da suka gabata, inda ta aiwatar da tsauraran manufofin rigakafi, da shawo kan cutar a lokacin da ake shan fama da ita, ta jure jarrabawar yaduwar annobar har sau biyar, kana da rage yawan wadanda suka nuna alamu masu tsanani ko kuma mace-mace a sakamakon cutar. Har ila yau, ta samu lokaci mai muhimmanci na nazarin magunguna, da alluran rigakafin cutar.

Kamar sauran kasashe, kasar Sin ma na bukatar wani lokaci na daidaitawa, wajen kyautata manufofin rigakafin cutar. Musamman yadda kasar Sin ke da yawan al’umma da yawan tsofaffi, don haka babu makawa, kasar na fuskantar wasu matsaloli, ciki har da karuwar adadin masu kamuwa da cutar, da masu bukatar magani. Amma duk da haka, gwamnatin kasar Sin ba ta taba yin kasa a gwiwa ba, wajen sanya himmar warware matsalolin ta. Bugu da kari, a cewar mai tsara shirye-shiryen documentary dan kasar Burtaniya Malcolm Clarke, wanda ya taba zama a kasar Sin tsawon shekaru uku da suka gabata, “Na kasance mai cin gajiyar kokarin da Sin ke yi na kare rayuka da lafiyar jama’a.”

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Daga yau 8 ga watan Janairu na shekarar bana, kasar Sin ta sassauta matakanta na yaki da cutar COVID-19 daga rukunin A zuwa rukunin B, don haka ta daina daukar matakan binciken cutar ba kan matafiya da kayayyaki dake shigowa daga ketare. Wannan shi ne kokarin da kasar Sin ta yi na baya-bayan nan, don inganta manufofin kandagarkin annobar bisa lokaci da yanayin da ake ciki, wanda hakan sauke nauyin al’ummar kasar ne, kuma yana taimakawa wajen farfado da tattalin arzikin duniya. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NDLEA Ta Yi Nasarar Kama Ƙwayoyi Da Tabar Wiwi Masu Yawan Gaske A Jihohi 4 A Nijeriya

Next Post

Ba Zan Kai ‘Ya’yana Karatu Waje Ba Idan Na Zama Gwamnan Kano – Abba Gida-Gida

Related

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

9 hours ago
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

10 hours ago
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden
Daga Birnin Sin

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

11 hours ago
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

12 hours ago
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

13 hours ago
Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021
Daga Birnin Sin

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

14 hours ago
Next Post
Abba Gida-Gida Ya Maka Shugaban APC Na Kano A Kotu Kan Kalaman Tunzura Mutane

Ba Zan Kai 'Ya'yana Karatu Waje Ba Idan Na Zama Gwamnan Kano - Abba Gida-Gida

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.