ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hamas: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Isra’ila Saboda Ƙin Amincewar Ƙasar Kan Tsagaita Buɗe Wuta

by Sulaiman
1 year ago
Isra'ila

An fara gudanar da gagarumar zanga-zanga a duk fadin kasar Isra’ila ranar Lahadi bayan mutuwar wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su a Gaza, inda jama’a ke ci gaba da nuna bacin ransu kan gazawar gwamnatin kasar wajen cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta domin ceto Isra’ilawan da aka yi garkuwa da su.

 

Kimanin mutane 500,000 ne a cewar kafofin yada labaran Isra’ila, sun fito kan tituna a biranen Jerusalem, Tel Aviv, da sauran garuruwa, suna kira ga Firaminista Benjamin Netanyahu da ya dauki kwararan matakai na dawo da sauran mutane 101 da aka yi garkuwa da su gida.

ADVERTISEMENT
  • Nijar Za Ta Fara Tattara Bayanan ‘Yan Ta’adda
  • Ya Zuwa Karshen Bara Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Ga Al’ummun Afirka Miliyan 230

A birnin Kudus, masu zanga-zangar sun rufe tituna tare da taruwa a wajen gidan firaministan da ke Tel Aviv inda masu zanga-zanga dauke da tutoci ke daga hotunan wadanda aka yi garkuwa da su.

 

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Hotunan talabijin sun kuma nuna yadda ‘yansanda ke amfani da motar ruwa a kan wadanda suka tare tituna, kuma kafafen yada labaran kasar sun bayar da rahoton kama mutane 29.

 

Tuni dai, Shugabannin jam’iyyar Kwadago ta kasar suka sanar da fara yajin aikin gama-gari na kwana daya a ranar Litinin.

 

Sojojin Isra’ila sun sanar da gano gawarwakin 6 daga wani rami da ke kudancin birnin Rafah da ke kudancin Gaza, a daidai lokacin da aka fara aikin rigakafin cutar shan inna a yankin Falasdinawa da ke fama da yaki da kuma tashin hankali a yammacin gabar kogin Jordan.

 

An mayar da gawarwakin da aka tsinto da suka hada da Carmel Gat, Hersh Goldberg-Polin, Eden Yerushalmi, Alexander Lobanov, Almog Sarusi da Ori Danino zuwa Isra’ila, kamar yadda kakakin rundunar Rear Admiral Daniel Hagari ya shaidawa manema labarai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Coas
Manyan Labarai

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina
Manyan Labarai

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP
Manyan Labarai

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
Next Post
ACF Ta Yaba Wa Tinubu Kan Amincewa Da Ziyarar Sulhu Da Shugaban Sojojin Nijeriya Ya Kai A Nijar 

ACF Ta Yaba Wa Tinubu Kan Amincewa Da Ziyarar Sulhu Da Shugaban Sojojin Nijeriya Ya Kai A Nijar 

LABARAI MASU NASABA

Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.