ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hamas: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Isra’ila Saboda Ƙin Amincewar Ƙasar Kan Tsagaita Buɗe Wuta

by Sulaiman
2 years ago
Isra'ila

An fara gudanar da gagarumar zanga-zanga a duk fadin kasar Isra’ila ranar Lahadi bayan mutuwar wasu mutane shida da aka yi garkuwa da su a Gaza, inda jama’a ke ci gaba da nuna bacin ransu kan gazawar gwamnatin kasar wajen cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta domin ceto Isra’ilawan da aka yi garkuwa da su.

 

Kimanin mutane 500,000 ne a cewar kafofin yada labaran Isra’ila, sun fito kan tituna a biranen Jerusalem, Tel Aviv, da sauran garuruwa, suna kira ga Firaminista Benjamin Netanyahu da ya dauki kwararan matakai na dawo da sauran mutane 101 da aka yi garkuwa da su gida.

ADVERTISEMENT
  • Nijar Za Ta Fara Tattara Bayanan ‘Yan Ta’adda
  • Ya Zuwa Karshen Bara Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Ga Al’ummun Afirka Miliyan 230

A birnin Kudus, masu zanga-zangar sun rufe tituna tare da taruwa a wajen gidan firaministan da ke Tel Aviv inda masu zanga-zanga dauke da tutoci ke daga hotunan wadanda aka yi garkuwa da su.

 

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

Hotunan talabijin sun kuma nuna yadda ‘yansanda ke amfani da motar ruwa a kan wadanda suka tare tituna, kuma kafafen yada labaran kasar sun bayar da rahoton kama mutane 29.

 

Tuni dai, Shugabannin jam’iyyar Kwadago ta kasar suka sanar da fara yajin aikin gama-gari na kwana daya a ranar Litinin.

 

Sojojin Isra’ila sun sanar da gano gawarwakin 6 daga wani rami da ke kudancin birnin Rafah da ke kudancin Gaza, a daidai lokacin da aka fara aikin rigakafin cutar shan inna a yankin Falasdinawa da ke fama da yaki da kuma tashin hankali a yammacin gabar kogin Jordan.

 

An mayar da gawarwakin da aka tsinto da suka hada da Carmel Gat, Hersh Goldberg-Polin, Eden Yerushalmi, Alexander Lobanov, Almog Sarusi da Ori Danino zuwa Isra’ila, kamar yadda kakakin rundunar Rear Admiral Daniel Hagari ya shaidawa manema labarai.

Isra'ila
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a
  • Sulaiman
    Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
  • Sulaiman
    Jagoran Majalisar Shugabancin Kasar Libya Ya Yi Fatan Ci Gaba Da Ingiza Dangantakar Kasarsa Da Sin

MASU ALAKA

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027
Manyan Labarai

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato
Manyan Labarai

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai
Manyan Labarai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Next Post
ACF Ta Yaba Wa Tinubu Kan Amincewa Da Ziyarar Sulhu Da Shugaban Sojojin Nijeriya Ya Kai A Nijar 

ACF Ta Yaba Wa Tinubu Kan Amincewa Da Ziyarar Sulhu Da Shugaban Sojojin Nijeriya Ya Kai A Nijar 

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026
Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

Ministoci Da Gwamnoni Za a Koma Kai Wa Hari Nan Gaba – Buratai

June 14, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.