• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hana Bahaya A Fili: Nijeriya Na Bukatar Ban-daki Miliyan 3.9 Duk Shekara –UNICEF

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Labarai
0
Hana Bahaya A Fili: Nijeriya Na Bukatar Ban-daki Miliyan 3.9 Duk Shekara –UNICEF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ta bayyana cewa Nijeriya na bukatar ban-daki miliyan 3.9, domin hana bahaya a fili nan da shekara ta 2025.

Babbar jami’ar tsaftace ruwa ta UNICEF, Misis Jane Beban ita ce ta bayyana haka lokacin da aka bude taron kwana biyu da ya shafi al’amuran masu sana’ar ban-daki a Abuja.

Misis Beban ta bayyana cewa yawan ban-dakin da ake ginawa kowace shekara tsakanin 180,000 zuwa 200,000 matsayin wadanda ba su isa ba.

Ta ce taron an yi shi ne lokacin da ya dace domin kuwa sana’ar gina ban-daki wata hanya ce ta kawo karshen matsalar da ake fuskanta a Nijeriya ta yin kashi a fili.

Ta ce kungiyoyi masu zaman kansu suna da gudunmawar da za su taka wajen ingantuwa da karfafa al’amauran tsafta a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

Beban ta kara jaddada cewa a shekarar 2021 karkashin tsarin WASH ko tsaftace ruwa an gano cewa mutane miliyan 48 ne suke bahaya a fili ba tare da suna da hanyar da za su tsaftace kansu ba, yayin da miliyan 95 ba su da wata hanya ta kusanta da al’amarin da ya shafi tsaftar kansu ko muhalli.

“Ana asarar kashi 1.3 ko Naira biliyan 455 kowace shekara saboda rashin samun ingantaccen al’amarin da ya shafi tsafta da kula da lafiya da yin abin da zai samar da karuwa a gaba.

 “Kowace dala guda da aka zuba a harkar da ta shafi ruwa da tsafta za ta samar da dala 3 zuwa 34.

“Nijeriya ba za ta ci gaba da tafiya da al’amura ba tare da abin da gaba za ta iya haifarwa ba, idan ba haka ba tana iya rasa cimma muradan ci gaba na shekarar 2025 ko 2030. Akwai bukatar daukar dukkan matakan da suka dace domin samun damar cimma muradun karni.

 “Kungiyoyi masu zaman kansu akwai bukatar su yi aiki kafada- kafada da gwamnatocin tarayya, jihohi, kananan hukumomi tare da kuma gundumomi domin samun damar zuba jari a tsarin ma’aikata”.

Babban Sakatariyar ta ma’aikatar albarkatun ruwa, Didi Walson-Jack ta nuna cewa da akwai tabbacin masu sana’ar ban-daki za su taimaka wa kokarin da gwamnati take yi na cimma muradun hana bahaya a fili.

Ta kara jaddada cewa Nijeriya a shirye take wajen shiga harkar duk da yake akwai tsada idan har ana bukatar samun babbar riba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ba-HayaBandakiNijeriyaUNICEF
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ina Son Kara Aure, Ko Me Yake Kawo Matsaloli Tsakanin Kishiyoyi Da Yadda Za A Magance?

Next Post

Shugaban Kasar Sin Ya Bukaci Lardin Jiangsu Da Ya Ja Ragamar Aiwatar Da Manufofin Bunkasa Zamanintar Da Kasar

Related

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

3 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

4 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

14 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

16 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

18 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

19 hours ago
Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Bukaci Lardin Jiangsu Da Ya Ja Ragamar Aiwatar Da Manufofin Bunkasa Zamanintar Da Kasar

Shugaban Kasar Sin Ya Bukaci Lardin Jiangsu Da Ya Ja Ragamar Aiwatar Da Manufofin Bunkasa Zamanintar Da Kasar

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.