• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hana Bahaya A Fili: Nijeriya Na Bukatar Ban-daki Miliyan 3.9 Duk Shekara –UNICEF

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Labarai
0
Hana Bahaya A Fili: Nijeriya Na Bukatar Ban-daki Miliyan 3.9 Duk Shekara –UNICEF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ta bayyana cewa Nijeriya na bukatar ban-daki miliyan 3.9, domin hana bahaya a fili nan da shekara ta 2025.

Babbar jami’ar tsaftace ruwa ta UNICEF, Misis Jane Beban ita ce ta bayyana haka lokacin da aka bude taron kwana biyu da ya shafi al’amuran masu sana’ar ban-daki a Abuja.

Misis Beban ta bayyana cewa yawan ban-dakin da ake ginawa kowace shekara tsakanin 180,000 zuwa 200,000 matsayin wadanda ba su isa ba.

Ta ce taron an yi shi ne lokacin da ya dace domin kuwa sana’ar gina ban-daki wata hanya ce ta kawo karshen matsalar da ake fuskanta a Nijeriya ta yin kashi a fili.

Ta ce kungiyoyi masu zaman kansu suna da gudunmawar da za su taka wajen ingantuwa da karfafa al’amauran tsafta a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Beban ta kara jaddada cewa a shekarar 2021 karkashin tsarin WASH ko tsaftace ruwa an gano cewa mutane miliyan 48 ne suke bahaya a fili ba tare da suna da hanyar da za su tsaftace kansu ba, yayin da miliyan 95 ba su da wata hanya ta kusanta da al’amarin da ya shafi tsaftar kansu ko muhalli.

“Ana asarar kashi 1.3 ko Naira biliyan 455 kowace shekara saboda rashin samun ingantaccen al’amarin da ya shafi tsafta da kula da lafiya da yin abin da zai samar da karuwa a gaba.

 “Kowace dala guda da aka zuba a harkar da ta shafi ruwa da tsafta za ta samar da dala 3 zuwa 34.

“Nijeriya ba za ta ci gaba da tafiya da al’amura ba tare da abin da gaba za ta iya haifarwa ba, idan ba haka ba tana iya rasa cimma muradan ci gaba na shekarar 2025 ko 2030. Akwai bukatar daukar dukkan matakan da suka dace domin samun damar cimma muradun karni.

 “Kungiyoyi masu zaman kansu akwai bukatar su yi aiki kafada- kafada da gwamnatocin tarayya, jihohi, kananan hukumomi tare da kuma gundumomi domin samun damar zuba jari a tsarin ma’aikata”.

Babban Sakatariyar ta ma’aikatar albarkatun ruwa, Didi Walson-Jack ta nuna cewa da akwai tabbacin masu sana’ar ban-daki za su taimaka wa kokarin da gwamnati take yi na cimma muradun hana bahaya a fili.

Ta kara jaddada cewa Nijeriya a shirye take wajen shiga harkar duk da yake akwai tsada idan har ana bukatar samun babbar riba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ba-HayaBandakiNijeriyaUNICEF
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ina Son Kara Aure, Ko Me Yake Kawo Matsaloli Tsakanin Kishiyoyi Da Yadda Za A Magance?

Next Post

Shugaban Kasar Sin Ya Bukaci Lardin Jiangsu Da Ya Ja Ragamar Aiwatar Da Manufofin Bunkasa Zamanintar Da Kasar

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

18 minutes ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

3 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

4 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

13 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

15 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

16 hours ago
Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Bukaci Lardin Jiangsu Da Ya Ja Ragamar Aiwatar Da Manufofin Bunkasa Zamanintar Da Kasar

Shugaban Kasar Sin Ya Bukaci Lardin Jiangsu Da Ya Ja Ragamar Aiwatar Da Manufofin Bunkasa Zamanintar Da Kasar

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.