ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hana Bahaya A Fili: Nijeriya Na Bukatar Ban-daki Miliyan 3.9 Duk Shekara –UNICEF

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Bahaya

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ta bayyana cewa Nijeriya na bukatar ban-daki miliyan 3.9, domin hana bahaya a fili nan da shekara ta 2025.

Babbar jami’ar tsaftace ruwa ta UNICEF, Misis Jane Beban ita ce ta bayyana haka lokacin da aka bude taron kwana biyu da ya shafi al’amuran masu sana’ar ban-daki a Abuja.

Misis Beban ta bayyana cewa yawan ban-dakin da ake ginawa kowace shekara tsakanin 180,000 zuwa 200,000 matsayin wadanda ba su isa ba.

ADVERTISEMENT

Ta ce taron an yi shi ne lokacin da ya dace domin kuwa sana’ar gina ban-daki wata hanya ce ta kawo karshen matsalar da ake fuskanta a Nijeriya ta yin kashi a fili.

Ta ce kungiyoyi masu zaman kansu suna da gudunmawar da za su taka wajen ingantuwa da karfafa al’amauran tsafta a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Beban ta kara jaddada cewa a shekarar 2021 karkashin tsarin WASH ko tsaftace ruwa an gano cewa mutane miliyan 48 ne suke bahaya a fili ba tare da suna da hanyar da za su tsaftace kansu ba, yayin da miliyan 95 ba su da wata hanya ta kusanta da al’amarin da ya shafi tsaftar kansu ko muhalli.

“Ana asarar kashi 1.3 ko Naira biliyan 455 kowace shekara saboda rashin samun ingantaccen al’amarin da ya shafi tsafta da kula da lafiya da yin abin da zai samar da karuwa a gaba.

 “Kowace dala guda da aka zuba a harkar da ta shafi ruwa da tsafta za ta samar da dala 3 zuwa 34.

“Nijeriya ba za ta ci gaba da tafiya da al’amura ba tare da abin da gaba za ta iya haifarwa ba, idan ba haka ba tana iya rasa cimma muradan ci gaba na shekarar 2025 ko 2030. Akwai bukatar daukar dukkan matakan da suka dace domin samun damar cimma muradun karni.

 “Kungiyoyi masu zaman kansu akwai bukatar su yi aiki kafada- kafada da gwamnatocin tarayya, jihohi, kananan hukumomi tare da kuma gundumomi domin samun damar zuba jari a tsarin ma’aikata”.

Babban Sakatariyar ta ma’aikatar albarkatun ruwa, Didi Walson-Jack ta nuna cewa da akwai tabbacin masu sana’ar ban-daki za su taimaka wa kokarin da gwamnati take yi na cimma muradun hana bahaya a fili.

Ta kara jaddada cewa Nijeriya a shirye take wajen shiga harkar duk da yake akwai tsada idan har ana bukatar samun babbar riba.

Bahaya
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Jihohi Suka Fara Ɗanɗana Ambaliyar Ruwa A Daminar Bana
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    ‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

MASU ALAKA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
Labarai

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Bukaci Lardin Jiangsu Da Ya Ja Ragamar Aiwatar Da Manufofin Bunkasa Zamanintar Da Kasar

Shugaban Kasar Sin Ya Bukaci Lardin Jiangsu Da Ya Ja Ragamar Aiwatar Da Manufofin Bunkasa Zamanintar Da Kasar

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.