• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hana Natasha Zaman Majalisa Barazana Ne Ga Dimokuraɗiyya — CLO

by Abubakar Sulaiman
3 months ago
Natasha

Ƙoƙarin hana Sanata Natasha Akpoti-Uduagha daga ci gaba da aiki a Majalisar Dattawa barazana ce ga cigaban dimokuraɗiyya a Nijeriya, in ji Kwamared Steve Aluko, wanda shi ne ko’odinetan ƙungiyar kare ‘yancin ɗan adam ta yankin Arewa ta Tsakiya (CLO).

Sanata Natasha ta rubuta wa Sufeto Janar na ƴansanda, inda ta sanar da niyyarta ta komawa bakin aiki, tare da roƙon a maido da jami’an tsaron da aka sa mata. Amma sai gashi a ranar Talata, jami’an tsaro sun hana ta shiga Majalisar Tarayya duk da wata hukuncin kotu da ta ba ta damar komawa kujerarta.

  • Natasha Ta Koma Majalisar Dattawa Duk Da Tsaurara Tsaro
  • ‘Ka Da Ki Kuskura Ki Zo Majalisar Tarayya’, Majalisar Dattawa Ta Sake Yi Wa Natasha Gargaɗi

Aluko ya bayyana hakan a wata hira da LEADERSHIP a Jos, babban birnin jihar Filato, inda ya ce wannan mataki yana ƙara bayyana gazawar Majalisar Dattawa ta 10 wajen kare tsarin mulki da doka. Ya ce abin da ke faruwa ba ya wakiltar muradun ƙasa, sai dai na wasu mutane da ke da wata manufa ta siyasa.

Ya zargi ofishin Sufeto Janar na ƴansanda da ƙin yin aiki da korafe-korafen da aka aika musu dangane da batun, inda ya ce hukumar ƴansanda ta gaza kare Sanata Natasha da tabbatar da ta koma bakin aiki lafiya bisa doka. A cewarsa, hana ta shiga majalisar “ba bisa ka’ida ba ne, kuma ya ci karo da hukuncin kotu da ya tabbatar da dawowarta.”

Aluko ya jaddada cewa, muddin babu wani sabon hukuncin kotu da ke soke wanda aka riga aka bayar, to babu wata hukuma ko mutum da zai hana ta komawa aiki. Ya ce wannan lamari ya nuna rashin mutunta kundin tsarin mulki, kuma zalunci ne ga mazabar da Sanata Natasha ke wakilta.

LABARAI MASU NASABA

Bankin Providus

Hukumar NASENI

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

Bankin Providus

October 25, 2025
Labarai

Hukumar NASENI

October 25, 2025
Labarai

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Next Post
Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

Zhao Leji Da Wang Huning Sun Gana Da Shugaban Majalisar Dattijan Kasar Madagascar

LABARAI MASU NASABA

Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025

Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

October 25, 2025
Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

October 25, 2025
An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC

An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.