ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanya Mafi Sauki Da Za A Magance Matsalar Tsaro A Katsina – Gamayyar Kungiyoyin Arewa

by El-Zaharadeen Umar
1 year ago
katsina

Babban kodinaita na gamayyar kungiyoyin arewa na Jihar Katsina, Habibu Ruma ya bayyana wasu hanyoyi da suke ganin idan gwamnatin Jihar Katsina ta yi amfani da su za a iya samun nasara kan matsalar tsaron da ta addibi jihar da yankin arewa baki daya.

Kodinaitan gamayyar kungiyoyin ya yi wannan karin haske ne a lokacin da suka shirya wani taro domin fadakar da ‘ya‘yan kungiyar halin da yanayin da tsaro ya samu kanshi a Jihar Katsina da kuma arewa baki daya.

  • Matsayar Ƙungiyar Sarakunan Arewa A Tsaya Kan Umarnin Kotu Kan Rikicin Sarki 2 A Kano
  • Mun Dukafa Kawo Karshen Matsalar Wuta A Arewa Maso Gabas – Gwamna Inuwa

Habibu wanda ya yi bitar cewa matsalar tsaro a Jihar Katsina da kuma arewacin Nijeriya ta kassara duk wani ci gaba a bangaren ilimi da haifar da jahilci da rashin shugabanci da shan miyagun kwayoyi wanda har gobe sune ake gani matsayin dalilin faruwar haka.

ADVERTISEMENT

Yana mai cewa farmakin da ‘yan bindiga suka kai wa sojojin Nijeriya a karamar hukumar Faskari wanda suka kashe sojoji 5 da raunata da dama, sannan kasa da awa 24 aka sake kai wani harin a garin ‘yar Malamai duk a Faskari tare da sace mutum fiye da mutane 80 da sace kayayyakin shaguna da kone gidaje abin takaici ne da zub da hawaye.

Ya bayyana cewa duk da irin kokarin da gwamnatin Jihar Katsina ta yi karkashin gwamna Malam Dikko Umar Radda, musamman samar da dakurun tsaro na C-Watch, sannan an samar da irinsa a Zamfara wato Askarawa da Sakkwato ya kara nuna yadda ake so a shawo kan wannan matsala.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

Sai dai ya yi bayanin cewa gamayyar kungiyoyin arewa da sauran kungiyoyin farar hula a Jihar Katsina suna kira da a yi amfani da sabbin hanyoyin sulhu tare da kara samar da wasu hanyoyi saboda yanayin da ake ciki yana bukatar hannu da yawa.

Haka kuma Habibu ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi kokari wajen sanya kowa cikin wannan al’amari domin samun nasara, ba wai ta rika tunzura ‘yan bindiga ba, kamar yadda ake gani a halin yanzu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026
Labarai

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani
Labarai

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Next Post
arewa

Jihohin Arewa Za Su Ware Kaso 5 Na Kasafi Don Taimaka Wa 'Yan Gudun Hijira

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

November 14, 2025
Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.