ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohin Arewa Za Su Ware Kaso 5 Na Kasafi Don Taimaka Wa ‘Yan Gudun Hijira

by Khalid Idris Doya
2 years ago
arewa

Gwamnonin jihohin Adamawa, Benuwai, Borno da Yobe sun sha alwashin ware kaso sama da biyar daga cikin kasafin kudin jihohinsu domin taimaka wa rayuwar ‘yan gudun hijira sama da miliyan hudu da suke zaman neman mafaka a jihohinsu.

Gwamnonin sun sha alwashin ne yayin wani taron kaddamar da shiri na musamman domin nemi mafita mai dorewa kan halin da ‘yan gudun hijira ke ciki da ya gudana a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

  • Taron Gwamnonin Arewa Maso Gabas Karo Na 10, Me Ya Kamata Ku Sani?
  • Mun Rage Barazanar Ƴan Bindiga Da 70% A Jihar Katsina – Gwamna Radda

Da take magana a yayin taron ta yanar gizo, mataimakiyar babban sakataren majalisar dinkin duniya, Amina Mohammed, ta ce lalubo bakin zaren shawo kan matsalolin na ‘yan gudun hijira na daga cikin muhimman abubuwan da ya kamata Nijeriya ta sanya a gaba kuma ita kanta majalisar dinkin duniya ta damu da lamarin.

ADVERTISEMENT

Ta lura kan cewa adadin ‘yan gudun hijira ya ninku a cikin shekaru goma da ya kai kusan mutum miliyan 76 da suke halin gudun hijira a fadin duniya.

“Sama da ‘yan Nijeriya miliyan hudu na neman mafita zuwa inda aka tilasta musu yin kaura na dole,” ta ce, tsarin a matakin farko zai ba da mafita kan yadda za a nemi hanyoyin magance matsalolin da suka shafi na mutanen.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Tun da farko a jawabinsa, mukaddashin babban sakataren majalisar dinkin duniya kuma mashawarci kan nemo mafita mai dorewa, Mista Robert Piper, ya jinjina wa irin azamar gwamnatin Nijeriya da shugabanninta wajen ganin sun zama kasa ta farko a cikin kasashe 15 wajen kaddamar da shirin neman mafita mai dorewa ga ‘yan gudun hijira.

Piper ya ce kaddamar da shirin wata alama ce da ke nuni da cewa tabbas ‘yan siyasan da suke kan mulki a yanzu sun himmatu wajen ganin sun taimaka wa ‘yan gudun hijira da nema musu mafita a Nijeriya. Ya ce, dabarbaru da hikimomin yadda za a bi duk suna kunshe cikin shirin.

Shi kuma a nasa bangaren, mataimakin shugaban kasar Nijeriya, Sanata Kashim Shettima, ya yi kira ne na samar da hadin guiwa a duniyance wajen ganin an shawo kan matsalolin ‘yan gudun hijara a Nijeriya.
Ya ce, gwamnatin tarayya ta himmatu ainun wajen ganin ta kyautata da kare rayuwar ‘yan gudun hijira.

Da yake kaddamar da shirin da za a aiwatar a jihohi hudu da suke arewa Adamawa, Benuwai, Borno da Yobe, Shettima ya ce, babu yadda za a yi gwamnati ta dage idonta daga kan ‘yan gudun hijira ko daina damuwa da matsalolinsu, a maimakon hakan ya tabbatar da cewa dole ne a kare rayuwar kowani dan kasa.

Shi kuma a nasa bangaren, gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya ce, gwamnatin jihar a shirye take dari bisa dari wajen aiwatar da shirin da aka tsara domin nemo mafita. Ya ce, gwamnatinsa za ta iya ware kaso mai tsoka fiye da yadda ake tsammani domin nasarar shirin.

Zulum ya ce, gwamnatinsa tana kokarin yadda za su maida ‘yan gudun hijira garuruwansu na asali domin ci gaba da gudanar da harkokin rayuwarsu.

Shi ma gwamna Jihar Benuwai, Hyacinth Alia ya ce, kaddamar da shirin zai taimaka sosai wajen kyautata rayuwa da jin dadin al’umman da suke jiharsa.

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya ce, sun maida hankali wajen gudanar da ayyukan da kai tsaye za su kyautata da inganta rayuwar al’ummarsu, don haka a shirye suke su mara wa shirin kyautata rayuwar ‘yan gudun hijira baya.

Arewa
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
iyakokin kasa

Na’urorin Kula Da Iyakokin Kasa Za Su Fara Aiki Ba Da Jimawa Ba – Ministan Cikin Gida

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.