• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyi 18 Na Rage Radadin Matsin Tattalin Da Ake Ciki

by Bello Hamza
1 year ago
Hanyoyi

A daidai lokacin da matasan Nijeriya ke gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwa da matsin tattalin arziki a Nijeriya, masana sun nuna cewa, zanga zangar ba zai dawo da tattalinarzikin kasa yaddayake a da a cikin gaggawa, saboda haka ya kamata al’umma su samar wa kansu hanyoyin ci gaba da fuskantar wadannan matsalolin Wakilinmu ya zakulo muku wasu shawarwari da dabaru da masana suka fitar wanda mutane za su iya amfani da su domin rage radadin matsin da ake fuskanta.

1. Idan wuri ba shi da nisa, to a daure a taka a kafa. Yin hakan zai kara lafiyar jiki da kuma kiyaye ‘yan kudade.

2. Akwai kayan abinci masu kosarwa da basu bukatar a dora su a wuta; kamar garin kwaki da sukari, da ‘yar gyada mai gishiri. Idan a inda kake akwai gurasa ita ma za ta kashe yunwa ba tare da an kashe kudade da yawa ba.

3. A rage yin baki da kuma kai ziyara har sai idan ya zama dole. Idan za a kai wa wani ziyara a rika sanar tun kafin lokacin ziyarar. A karfafa zumunci ta wayar salula.

4. Idan za a dafa shinkafa a jika ta sosai, kafin a dora ta a wuta. Sannan yayin da take kan wuta a sa ido sosai.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

5. A guji barnar kudi wajen sayen naman miya. Amfani da wake ko ganye kamar alayyaho yafi rahusa da kuma kara lafiyar jiki.

6. A rika dora zogale, ko tafasa a abinci suna hanzarta koshi da kara lafiya.

7. Duk kwan lantarki ko kyandir a tabbatar an kashe su, kada a kunna sai daidai lokacin da ake bukatar haske.

8. Indomie tana da sauki da kuma rahusa. Amma a kiyaye gishirin da ke cikinta, domin yana da illa.

9. A rika amfani da mizani ko sikeli wajen tantance kayan abincin da za a yi amfani ko za a dafa a gida. Hakan zai rage barna da kuma tabbatar abin da aka dafa daidai yake da bukata.

10. Ba dole ba ne a ci abinci sau 3 a kowacce rana, idan har babu yunwa ko sau biyu 2 kawai aka ci abinci babu laifi.

11. Gero, dawa da masara suna bukatar hidima sosai kafin su zama abinci. A guje su dukka, sai dai idan babu wani zabin.

12. Danwake yana da nagarta wajen kashe yunwa, kuma ba ya bukatar hidima sosai.

13. Dumame yana da albarka. Idan abinci ya yi saura a tanade shi domin da safe a yi dumame.

14. Idan akwai beraye a gida a tabbatar an halaka su da guba mai karfi. Baraye suna yin barnar kayan abinci da kuma sacewa.

15. Idan har kana da wayar salula baka bukatar agogo; idan kana da agogo ka sayar a sayo wani abu mai amfani.

16. A dakatar dayin sabuwar sutura, na dan wani lokaci, sai dai idan ya zama dole. A takaita yawan yin sutura. Kufta tana da karko da jimawa.

17. Wajen girki, amfani da gawayi yafi sauki.

18. Idan maigida ya je kasuwa ya tarar farashin kayan abinci ya karu, koda kadan ne, to a sanar da uwargida, domin ita ma ta san halin da ake ciki. Haka zai taimaka wajen tsumin abinda ake da shi da kuma kyautata tattalin arzikin iyali.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

October 17, 2025
sallah
Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

October 11, 2025
Next Post
Manzon Musamman Na Xi Jinping Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Kasar Mauritania

Manzon Musamman Na Xi Jinping Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Kasar Mauritania

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.