ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hanyoyi 18 Na Rage Radadin Matsin Tattalin Da Ake Ciki

by Bello Hamza
2 years ago
Hanyoyi

A daidai lokacin da matasan Nijeriya ke gudanar da zanga-zangar tsadar rayuwa da matsin tattalin arziki a Nijeriya, masana sun nuna cewa, zanga zangar ba zai dawo da tattalinarzikin kasa yaddayake a da a cikin gaggawa, saboda haka ya kamata al’umma su samar wa kansu hanyoyin ci gaba da fuskantar wadannan matsalolin Wakilinmu ya zakulo muku wasu shawarwari da dabaru da masana suka fitar wanda mutane za su iya amfani da su domin rage radadin matsin da ake fuskanta.

1. Idan wuri ba shi da nisa, to a daure a taka a kafa. Yin hakan zai kara lafiyar jiki da kuma kiyaye ‘yan kudade.

2. Akwai kayan abinci masu kosarwa da basu bukatar a dora su a wuta; kamar garin kwaki da sukari, da ‘yar gyada mai gishiri. Idan a inda kake akwai gurasa ita ma za ta kashe yunwa ba tare da an kashe kudade da yawa ba.

ADVERTISEMENT

3. A rage yin baki da kuma kai ziyara har sai idan ya zama dole. Idan za a kai wa wani ziyara a rika sanar tun kafin lokacin ziyarar. A karfafa zumunci ta wayar salula.

4. Idan za a dafa shinkafa a jika ta sosai, kafin a dora ta a wuta. Sannan yayin da take kan wuta a sa ido sosai.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

5. A guji barnar kudi wajen sayen naman miya. Amfani da wake ko ganye kamar alayyaho yafi rahusa da kuma kara lafiyar jiki.

6. A rika dora zogale, ko tafasa a abinci suna hanzarta koshi da kara lafiya.

7. Duk kwan lantarki ko kyandir a tabbatar an kashe su, kada a kunna sai daidai lokacin da ake bukatar haske.

8. Indomie tana da sauki da kuma rahusa. Amma a kiyaye gishirin da ke cikinta, domin yana da illa.

9. A rika amfani da mizani ko sikeli wajen tantance kayan abincin da za a yi amfani ko za a dafa a gida. Hakan zai rage barna da kuma tabbatar abin da aka dafa daidai yake da bukata.

10. Ba dole ba ne a ci abinci sau 3 a kowacce rana, idan har babu yunwa ko sau biyu 2 kawai aka ci abinci babu laifi.

11. Gero, dawa da masara suna bukatar hidima sosai kafin su zama abinci. A guje su dukka, sai dai idan babu wani zabin.

12. Danwake yana da nagarta wajen kashe yunwa, kuma ba ya bukatar hidima sosai.

13. Dumame yana da albarka. Idan abinci ya yi saura a tanade shi domin da safe a yi dumame.

14. Idan akwai beraye a gida a tabbatar an halaka su da guba mai karfi. Baraye suna yin barnar kayan abinci da kuma sacewa.

15. Idan har kana da wayar salula baka bukatar agogo; idan kana da agogo ka sayar a sayo wani abu mai amfani.

16. A dakatar dayin sabuwar sutura, na dan wani lokaci, sai dai idan ya zama dole. A takaita yawan yin sutura. Kufta tana da karko da jimawa.

17. Wajen girki, amfani da gawayi yafi sauki.

18. Idan maigida ya je kasuwa ya tarar farashin kayan abinci ya karu, koda kadan ne, to a sanar da uwargida, domin ita ma ta san halin da ake ciki. Haka zai taimaka wajen tsumin abinda ake da shi da kuma kyautata tattalin arzikin iyali.

Hanyoyi
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Manzon Musamman Na Xi Jinping Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Kasar Mauritania

Manzon Musamman Na Xi Jinping Ya Halarci Bikin Rantsar Da Shugaban Kasar Mauritania

LABARAI MASU NASABA

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.