• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Kullum Babbar Kasa, Ita Ce Mai Kulawa Da Kanana

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Kasa

Yayin wani zaman Kwamitin Sulhu na MDD don gane da nazarin halin da ake ciki a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo, mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Geng Shuang, ya jaddada kasa da kasa su goyi bayan dakatar da bude wuta, da kawo karshen dauki ba dadi da kungiyoyi masu dauke da makamai ke yi a kasar.

Yanayin da Jamhuriyar Demokradiyyar Congo ke ciki, batu ne mai tayar da hankali ganin yadda kasar ta shafe sama da shekaru 30 tana fama da rikici, inda kuma a baya-bayan nan yanayin ya kara tsanani. Ba sai an fada ba, kowa ya san illar da rikici ke haifarwa, kama daga rashin matsuguni da na abinci, zuwa rashin ci gaba da sauransu, bare irin wannan rikici da ya ki ci ya ki cinyewa.

  • Liu Guozhong Ya Halarci Bikin Bude Taron Dandalin Hadin Gwiwar Gwamnatocin Kananan Hukumomin Sin Da Afrika
  • Li Qiang Ya Taya Keir Starmer Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Birtaniya

A cewar Geng Shuang, cikin watanni 3 kacal, dakarun kungiyoyi masu dauke da makamai sun hallaka sama da fararen hula 500, kana tashe-tashen hankula sun tilasawa kimanin mutane miliyan 7.3 rabuwa da muhallansu. Wannan kadai ya isa tunatar da al’ummar duniya cewa, wannan kasa da jama’arta na matukar bukatar dauki.

Sai dai a halin yanzu, wasu manyan kasashen duniya sun fi mayar da hankalinsu ga yada jita-jita da babakere, sun manta da nauyin da ya rataya a wuyansu na taimakawa juna, musammam kasashe masu karamin karfi. Maimakon taimakawa irin wadannan kasashe, sai ake mayar da hankali wajen abubuwa marasa muhimmanci.

Duk wanda ke bin yanayin harkokin duniya, zai yarda da cewa, kasar Sin ce kullum kan tuna da yanayin da kasashen Afrika ke ciki, kuma ita ce kullum ke tsaya musu da neman hanyoyin da za su warware matsalolinsu da kansu, ba tare da ta gindaya musu wasu sharudda na siyasa ko tsoma bakin cikin harkokinsu na gida ba. Wannan dalili ne ya sa a kullum nake kiran kasar Sin da babbar kasa da ta san ciwon kanta, kuma mai kulawa da na kasa da ita, duk da cewa ita ma tana da aiki a gabanta na raya tattalin arziki da zamantakewar al’ummarta, ba ta taba mantawa da taimakawa kasashe mabukata. Duk yadda mutum ya kai ga son zuciya ko yin karya, ba zai taba iya karyata manufar taimakon Sin ga kasashen Afrika, wato niyyarta na ganin sun samu ci gaba da zaman lafiya.

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Fatan ita ce, kasashen duniya za su amsa kira, su kuma mayar da hankali kan abubuwa mafiya muhimmanci da duniya ke bukata, don ganin jama’a sun rayu cikin kwanciyar hankali da wadata, domin hannu daya, ba ya daukar jinka-wato kasar Sin kadai, ba za ta iya daukar nauyin daidaita matsalolin duniya baki daya ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 
Daga Birnin Sin

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba
Daga Birnin Sin

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Next Post
Majalisa Zata Miƙawa Shugaban Ƙasa Ƙudurin Dokar Kafa Hukumar Cigaban Arewa Maso Yamma

Majalisa Zata Miƙawa Shugaban Ƙasa Ƙudurin Dokar Kafa Hukumar Cigaban Arewa Maso Yamma

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.