• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Kullum Babbar Kasa, Ita Ce Mai Kulawa Da Kanana

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Har Kullum Babbar Kasa, Ita Ce Mai Kulawa Da Kanana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin wani zaman Kwamitin Sulhu na MDD don gane da nazarin halin da ake ciki a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo, mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Geng Shuang, ya jaddada kasa da kasa su goyi bayan dakatar da bude wuta, da kawo karshen dauki ba dadi da kungiyoyi masu dauke da makamai ke yi a kasar.

Yanayin da Jamhuriyar Demokradiyyar Congo ke ciki, batu ne mai tayar da hankali ganin yadda kasar ta shafe sama da shekaru 30 tana fama da rikici, inda kuma a baya-bayan nan yanayin ya kara tsanani. Ba sai an fada ba, kowa ya san illar da rikici ke haifarwa, kama daga rashin matsuguni da na abinci, zuwa rashin ci gaba da sauransu, bare irin wannan rikici da ya ki ci ya ki cinyewa.

  • Liu Guozhong Ya Halarci Bikin Bude Taron Dandalin Hadin Gwiwar Gwamnatocin Kananan Hukumomin Sin Da Afrika
  • Li Qiang Ya Taya Keir Starmer Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Birtaniya

A cewar Geng Shuang, cikin watanni 3 kacal, dakarun kungiyoyi masu dauke da makamai sun hallaka sama da fararen hula 500, kana tashe-tashen hankula sun tilasawa kimanin mutane miliyan 7.3 rabuwa da muhallansu. Wannan kadai ya isa tunatar da al’ummar duniya cewa, wannan kasa da jama’arta na matukar bukatar dauki.

Sai dai a halin yanzu, wasu manyan kasashen duniya sun fi mayar da hankalinsu ga yada jita-jita da babakere, sun manta da nauyin da ya rataya a wuyansu na taimakawa juna, musammam kasashe masu karamin karfi. Maimakon taimakawa irin wadannan kasashe, sai ake mayar da hankali wajen abubuwa marasa muhimmanci.

Duk wanda ke bin yanayin harkokin duniya, zai yarda da cewa, kasar Sin ce kullum kan tuna da yanayin da kasashen Afrika ke ciki, kuma ita ce kullum ke tsaya musu da neman hanyoyin da za su warware matsalolinsu da kansu, ba tare da ta gindaya musu wasu sharudda na siyasa ko tsoma bakin cikin harkokinsu na gida ba. Wannan dalili ne ya sa a kullum nake kiran kasar Sin da babbar kasa da ta san ciwon kanta, kuma mai kulawa da na kasa da ita, duk da cewa ita ma tana da aiki a gabanta na raya tattalin arziki da zamantakewar al’ummarta, ba ta taba mantawa da taimakawa kasashe mabukata. Duk yadda mutum ya kai ga son zuciya ko yin karya, ba zai taba iya karyata manufar taimakon Sin ga kasashen Afrika, wato niyyarta na ganin sun samu ci gaba da zaman lafiya.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Fatan ita ce, kasashen duniya za su amsa kira, su kuma mayar da hankali kan abubuwa mafiya muhimmanci da duniya ke bukata, don ganin jama’a sun rayu cikin kwanciyar hankali da wadata, domin hannu daya, ba ya daukar jinka-wato kasar Sin kadai, ba za ta iya daukar nauyin daidaita matsalolin duniya baki daya ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JapanLi QiangSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ku Kammala Ayyukan Hanyoyi Cikin Watanni Uku Ko In Dakatar da Kwangilar – Ministan Aiyuka

Next Post

Majalisa Zata Miƙawa Shugaban Ƙasa Ƙudurin Dokar Kafa Hukumar Cigaban Arewa Maso Yamma

Related

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

51 minutes ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

2 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

3 hours ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

5 hours ago
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

23 hours ago
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

24 hours ago
Next Post
Majalisa Zata Miƙawa Shugaban Ƙasa Ƙudurin Dokar Kafa Hukumar Cigaban Arewa Maso Yamma

Majalisa Zata Miƙawa Shugaban Ƙasa Ƙudurin Dokar Kafa Hukumar Cigaban Arewa Maso Yamma

LABARAI MASU NASABA

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.