• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Kullum Babbar Kasa, Ita Ce Mai Kulawa Da Kanana

by Sulaiman and CGTN Hausa
12 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Har Kullum Babbar Kasa, Ita Ce Mai Kulawa Da Kanana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin wani zaman Kwamitin Sulhu na MDD don gane da nazarin halin da ake ciki a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo, mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Geng Shuang, ya jaddada kasa da kasa su goyi bayan dakatar da bude wuta, da kawo karshen dauki ba dadi da kungiyoyi masu dauke da makamai ke yi a kasar.

Yanayin da Jamhuriyar Demokradiyyar Congo ke ciki, batu ne mai tayar da hankali ganin yadda kasar ta shafe sama da shekaru 30 tana fama da rikici, inda kuma a baya-bayan nan yanayin ya kara tsanani. Ba sai an fada ba, kowa ya san illar da rikici ke haifarwa, kama daga rashin matsuguni da na abinci, zuwa rashin ci gaba da sauransu, bare irin wannan rikici da ya ki ci ya ki cinyewa.

  • Liu Guozhong Ya Halarci Bikin Bude Taron Dandalin Hadin Gwiwar Gwamnatocin Kananan Hukumomin Sin Da Afrika
  • Li Qiang Ya Taya Keir Starmer Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Birtaniya

A cewar Geng Shuang, cikin watanni 3 kacal, dakarun kungiyoyi masu dauke da makamai sun hallaka sama da fararen hula 500, kana tashe-tashen hankula sun tilasawa kimanin mutane miliyan 7.3 rabuwa da muhallansu. Wannan kadai ya isa tunatar da al’ummar duniya cewa, wannan kasa da jama’arta na matukar bukatar dauki.

Sai dai a halin yanzu, wasu manyan kasashen duniya sun fi mayar da hankalinsu ga yada jita-jita da babakere, sun manta da nauyin da ya rataya a wuyansu na taimakawa juna, musammam kasashe masu karamin karfi. Maimakon taimakawa irin wadannan kasashe, sai ake mayar da hankali wajen abubuwa marasa muhimmanci.

Duk wanda ke bin yanayin harkokin duniya, zai yarda da cewa, kasar Sin ce kullum kan tuna da yanayin da kasashen Afrika ke ciki, kuma ita ce kullum ke tsaya musu da neman hanyoyin da za su warware matsalolinsu da kansu, ba tare da ta gindaya musu wasu sharudda na siyasa ko tsoma bakin cikin harkokinsu na gida ba. Wannan dalili ne ya sa a kullum nake kiran kasar Sin da babbar kasa da ta san ciwon kanta, kuma mai kulawa da na kasa da ita, duk da cewa ita ma tana da aiki a gabanta na raya tattalin arziki da zamantakewar al’ummarta, ba ta taba mantawa da taimakawa kasashe mabukata. Duk yadda mutum ya kai ga son zuciya ko yin karya, ba zai taba iya karyata manufar taimakon Sin ga kasashen Afrika, wato niyyarta na ganin sun samu ci gaba da zaman lafiya.

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

Fatan ita ce, kasashen duniya za su amsa kira, su kuma mayar da hankali kan abubuwa mafiya muhimmanci da duniya ke bukata, don ganin jama’a sun rayu cikin kwanciyar hankali da wadata, domin hannu daya, ba ya daukar jinka-wato kasar Sin kadai, ba za ta iya daukar nauyin daidaita matsalolin duniya baki daya ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JapanLi QiangSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ku Kammala Ayyukan Hanyoyi Cikin Watanni Uku Ko In Dakatar da Kwangilar – Ministan Aiyuka

Next Post

Majalisa Zata Miƙawa Shugaban Ƙasa Ƙudurin Dokar Kafa Hukumar Cigaban Arewa Maso Yamma

Related

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

6 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Daga Birnin Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

7 hours ago
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

8 hours ago
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

9 hours ago
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

10 hours ago
Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

11 hours ago
Next Post
Majalisa Zata Miƙawa Shugaban Ƙasa Ƙudurin Dokar Kafa Hukumar Cigaban Arewa Maso Yamma

Majalisa Zata Miƙawa Shugaban Ƙasa Ƙudurin Dokar Kafa Hukumar Cigaban Arewa Maso Yamma

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.