• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ba A Kammala Kwangilar Dakin Karatu Da Aka Bayar Shekara 18 Ba

by Idris Aliyu Daudawa
11 months ago
in Ilimi, Labarai
0
Har Yanzu Ba A Kammala Kwangilar Dakin Karatu Da Aka Bayar Shekara 18 Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Aiki Ya Ki Ci Ya Ki Cinye Wa

Duk da yake gwamnati ta sha daukar alkawura na kammala aikin dakin karatu na kasa, wanda ya tsaya fiye da shekara 18, yayin da kayan da aka sa wajen fara ginin suka fara lalacewa.

Dakin karatun yana a Fuloti mai namba 35, Cadastral Business District a cikin babban birnin tarayya Abuja, tun farko an ba kamfanin Reynolds Construction Company kwangilar a shekarar 2006 lokacin mulkin tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo.

  • Zanga-zanga: Hukumar DSS Ta Kama Jagoran #EndbadGovernance A Abuja
  • Ƴansanda 2 Sun Mutu, 3 Sun Jikkata Bayan Arangama Da Ƴan Shi’a A Abuja

A lokacin an ba da kwangilar a kan kudi naira bilyan 8. Da milyan dari tara, wanda aka sa ran za a kammala shi cikin shekara hudu.

Binciken da LEADERSHIP ta yi ya gano ranar Litinin ta wannan makon aka cika shekara fiye da 18 tun lokacin da aka ba da kwangilar gina dakin karatun sai dai duk da hakan babu wasu alamu da suka nuna ana samun wani ci gaba dangane da kammala ita kwangilar.Fiye da kusan shekara da bada kwangilar, har ila yau ta kasance babu wasu alamun da ke nuna ana ci gaba da aikin.

Labarai Masu Nasaba

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Bayan an kasa kammala aikin sai gwamnatin tarayya ta sake ba da kwangilar a watan Maris shekarar 2010 inda aka bada wata 21 na lokacin da za a kammala kwangilar, kan kudi Naira bilyan 49.6. Duk da hakan babu wani abinda ke nuna akwai wani ci gaba

Binciken da aka yi ya nuna cewa matsalar lamarin kudin kwangilar yana da nasaba ne da yadda dala take kara tin tsada, da sauran wasu abubuwa, ya sa abinda ya hadu da matsala ga gwamnatocin da suka gabata, su sake zama da ‘yan kwangila domin a kammala aikin.

Kafin ya mika wa Shugaban kasa Bola Tinubu mulki, tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari ta amince da amsar aikin da kuma samar da kudadi da hukumar kula da ilimin manyan makarantu (TETFUND).

Lokacin da Ministan ilimi Farfesa Tahir Mamman ya fara aiki a matsayin Ministan ilimi a shekarar 2023, ya yi alkawarin zai ci gaba da kuma kammala aikin nan da shekara ta 2025.

Mamman ya ba da tabbacin cewar dan kwangilar da yake aikin zai dawo wurin, domin ya kammala aikin.

Ya ce“Wannan aikin yana da matukar amfani ga Nijeriya, ga shi kuma ba a kammala shi ba abin ya kusa shekara 20. Mun san muhimmancin dakin karatu, ba wa ma maganar dakin karatu na kasa ba. Don haka matakin da ya dace duk wanda yake da abinda zai yi dangane da wannan aiki, to ya dawo wurin aiki.

“Akwai matsaloli nan da can, amma za a kammala aikin cikin kusan wata 21. Muna yin kira da kamfanin da aka ba kwangilar, ya kammala aikin, saboda aikin ya dauki lokaci mai tsawo, don haka aiki irin wannan bai kamata ayi ta tafiyar Hawainiya ba.

“Don haka koma menene matsalar aikin, mun dauki niyyar kammala shi kamar yadda Ministan ya furta shekara daya data gabata.

Sai dai kuma wakilinmu wanda ya ziyarci wurin bada dadewa ba ya gano bai lura da wata alama ba ko alamun da za su nuna ana samun cigaba ba dangane da aikin dakin karatu, yayin da ziyarar da aka kai wurin da ake aikin ba wani abinda zai burge wanda ya je wurin.

Wannan aikin da aka fara ba a kammala ba ya jawo maganganu daban-daban daga dalibai, masu hrakar koyar da dalibai, inda suke kiran daukar mataki ba da dadewa ba, domin kammala shi saboda ya amfani al’ummar yanzu tare da wadanda za su kasance nan gaba.

A hirar da suka yi da LEADERSHIP, daliban Nijeriya a karkashin inuwar kungiyar dalibai ta kasa (NANS) da masu ruwa da tsaki daban- daban sun yi kira da a dauki matakin gaggawa domin a kammala ginin dakin karatu na kasa domin kuwa aikin ya dade ba a kammala gina shi ba.Ta nuna rashin jin dadinta akan cewar aikin ya tsaya shekaraIt 18 duk kuwa da yake gwamna tocin da suka shude sun yi alkawarin yin hakan.

Da yake furta albarkacin bakinsa jami’in hulda da jama’a na kungiyar Komrade Gundu Mimidoo Joy yace da aikin kowa yana yi ma shi Kallon wuri ne da zai amfani al’ummar Nijeriya musamman ma wadanda su masana ilimi ne, amma yanzu ya kasance wani wurin da aka yi watsi da shi ba tare dayin la’akarin ci bayan ilimi bane ba.

“Dalibai na yi ma shi aikin wani abu da yake da muhimmanci wajen cigaban lamarin koyarwa domin,a samu ilimi mai inganci.Dakatar da shi abin ya wakilci gazawar gwamnati ta ba ilimi kulawar data kamata.Shi yasa wannan tsayawar aikin ya kara bada gudunmawa ta bangaren lalacewar ko rashin ingancin yadda makarantu suke a fadin tarayyar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IlimiKaratuLibrary
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bayyana Matsaya Game Da Wasu Muhimman Batutuwa Biyowa Bayan Ziyarar Sullivan A Kasar

Next Post

An Kashe Dalibai 3, An Raunata Wani A Harin Da Boko Haram Ta Kai Makarantar ‘Yan Shi’a A Yobe

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

10 hours ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

11 hours ago
Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar É—orewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
Labarai

Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar É—orewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista

16 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

18 hours ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

19 hours ago
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
Manyan Labarai

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

21 hours ago
Next Post
An Kashe Dalibai 3, An Raunata Wani A Harin Da Boko Haram Ta Kai Makarantar ‘Yan Shi’a A Yobe

An Kashe Dalibai 3, An Raunata Wani A Harin Da Boko Haram Ta Kai Makarantar 'Yan Shi'a A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi HaÉ—in Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi HaÉ—in Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto DimokuraÉ—iyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.