ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ba A Kammala Kwangilar Dakin Karatu Da Aka Bayar Shekara 18 Ba

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Kwangila

Aiki Ya Ki Ci Ya Ki Cinye Wa

Duk da yake gwamnati ta sha daukar alkawura na kammala aikin dakin karatu na kasa, wanda ya tsaya fiye da shekara 18, yayin da kayan da aka sa wajen fara ginin suka fara lalacewa.

Dakin karatun yana a Fuloti mai namba 35, Cadastral Business District a cikin babban birnin tarayya Abuja, tun farko an ba kamfanin Reynolds Construction Company kwangilar a shekarar 2006 lokacin mulkin tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo.

ADVERTISEMENT
  • Zanga-zanga: Hukumar DSS Ta Kama Jagoran #EndbadGovernance A Abuja
  • Ƴansanda 2 Sun Mutu, 3 Sun Jikkata Bayan Arangama Da Ƴan Shi’a A Abuja

A lokacin an ba da kwangilar a kan kudi naira bilyan 8. Da milyan dari tara, wanda aka sa ran za a kammala shi cikin shekara hudu.

Binciken da LEADERSHIP ta yi ya gano ranar Litinin ta wannan makon aka cika shekara fiye da 18 tun lokacin da aka ba da kwangilar gina dakin karatun sai dai duk da hakan babu wasu alamu da suka nuna ana samun wani ci gaba dangane da kammala ita kwangilar.Fiye da kusan shekara da bada kwangilar, har ila yau ta kasance babu wasu alamun da ke nuna ana ci gaba da aikin.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Bayan an kasa kammala aikin sai gwamnatin tarayya ta sake ba da kwangilar a watan Maris shekarar 2010 inda aka bada wata 21 na lokacin da za a kammala kwangilar, kan kudi Naira bilyan 49.6. Duk da hakan babu wani abinda ke nuna akwai wani ci gaba

Binciken da aka yi ya nuna cewa matsalar lamarin kudin kwangilar yana da nasaba ne da yadda dala take kara tin tsada, da sauran wasu abubuwa, ya sa abinda ya hadu da matsala ga gwamnatocin da suka gabata, su sake zama da ‘yan kwangila domin a kammala aikin.

Kafin ya mika wa Shugaban kasa Bola Tinubu mulki, tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari ta amince da amsar aikin da kuma samar da kudadi da hukumar kula da ilimin manyan makarantu (TETFUND).

Lokacin da Ministan ilimi Farfesa Tahir Mamman ya fara aiki a matsayin Ministan ilimi a shekarar 2023, ya yi alkawarin zai ci gaba da kuma kammala aikin nan da shekara ta 2025.

Mamman ya ba da tabbacin cewar dan kwangilar da yake aikin zai dawo wurin, domin ya kammala aikin.

Ya ce“Wannan aikin yana da matukar amfani ga Nijeriya, ga shi kuma ba a kammala shi ba abin ya kusa shekara 20. Mun san muhimmancin dakin karatu, ba wa ma maganar dakin karatu na kasa ba. Don haka matakin da ya dace duk wanda yake da abinda zai yi dangane da wannan aiki, to ya dawo wurin aiki.

“Akwai matsaloli nan da can, amma za a kammala aikin cikin kusan wata 21. Muna yin kira da kamfanin da aka ba kwangilar, ya kammala aikin, saboda aikin ya dauki lokaci mai tsawo, don haka aiki irin wannan bai kamata ayi ta tafiyar Hawainiya ba.

“Don haka koma menene matsalar aikin, mun dauki niyyar kammala shi kamar yadda Ministan ya furta shekara daya data gabata.

Sai dai kuma wakilinmu wanda ya ziyarci wurin bada dadewa ba ya gano bai lura da wata alama ba ko alamun da za su nuna ana samun cigaba ba dangane da aikin dakin karatu, yayin da ziyarar da aka kai wurin da ake aikin ba wani abinda zai burge wanda ya je wurin.

Wannan aikin da aka fara ba a kammala ba ya jawo maganganu daban-daban daga dalibai, masu hrakar koyar da dalibai, inda suke kiran daukar mataki ba da dadewa ba, domin kammala shi saboda ya amfani al’ummar yanzu tare da wadanda za su kasance nan gaba.

A hirar da suka yi da LEADERSHIP, daliban Nijeriya a karkashin inuwar kungiyar dalibai ta kasa (NANS) da masu ruwa da tsaki daban- daban sun yi kira da a dauki matakin gaggawa domin a kammala ginin dakin karatu na kasa domin kuwa aikin ya dade ba a kammala gina shi ba.Ta nuna rashin jin dadinta akan cewar aikin ya tsaya shekaraIt 18 duk kuwa da yake gwamna tocin da suka shude sun yi alkawarin yin hakan.

Da yake furta albarkacin bakinsa jami’in hulda da jama’a na kungiyar Komrade Gundu Mimidoo Joy yace da aikin kowa yana yi ma shi Kallon wuri ne da zai amfani al’ummar Nijeriya musamman ma wadanda su masana ilimi ne, amma yanzu ya kasance wani wurin da aka yi watsi da shi ba tare dayin la’akarin ci bayan ilimi bane ba.

“Dalibai na yi ma shi aikin wani abu da yake da muhimmanci wajen cigaban lamarin koyarwa domin,a samu ilimi mai inganci.Dakatar da shi abin ya wakilci gazawar gwamnati ta ba ilimi kulawar data kamata.Shi yasa wannan tsayawar aikin ya kara bada gudunmawa ta bangaren lalacewar ko rashin ingancin yadda makarantu suke a fadin tarayyar Nijeriya.

Kwangila
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
An Kashe Dalibai 3, An Raunata Wani A Harin Da Boko Haram Ta Kai Makarantar ‘Yan Shi’a A Yobe

An Kashe Dalibai 3, An Raunata Wani A Harin Da Boko Haram Ta Kai Makarantar 'Yan Shi'a A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.