ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ba A Kammala Kwangilar Dakin Karatu Da Aka Bayar Shekara 18 Ba

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Kwangila

Aiki Ya Ki Ci Ya Ki Cinye Wa

Duk da yake gwamnati ta sha daukar alkawura na kammala aikin dakin karatu na kasa, wanda ya tsaya fiye da shekara 18, yayin da kayan da aka sa wajen fara ginin suka fara lalacewa.

Dakin karatun yana a Fuloti mai namba 35, Cadastral Business District a cikin babban birnin tarayya Abuja, tun farko an ba kamfanin Reynolds Construction Company kwangilar a shekarar 2006 lokacin mulkin tsohon Shugaban kasa Olusegun Obasanjo.

ADVERTISEMENT
  • Zanga-zanga: Hukumar DSS Ta Kama Jagoran #EndbadGovernance A Abuja
  • Ƴansanda 2 Sun Mutu, 3 Sun Jikkata Bayan Arangama Da Ƴan Shi’a A Abuja

A lokacin an ba da kwangilar a kan kudi naira bilyan 8. Da milyan dari tara, wanda aka sa ran za a kammala shi cikin shekara hudu.

Binciken da LEADERSHIP ta yi ya gano ranar Litinin ta wannan makon aka cika shekara fiye da 18 tun lokacin da aka ba da kwangilar gina dakin karatun sai dai duk da hakan babu wasu alamu da suka nuna ana samun wani ci gaba dangane da kammala ita kwangilar.Fiye da kusan shekara da bada kwangilar, har ila yau ta kasance babu wasu alamun da ke nuna ana ci gaba da aikin.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Bayan an kasa kammala aikin sai gwamnatin tarayya ta sake ba da kwangilar a watan Maris shekarar 2010 inda aka bada wata 21 na lokacin da za a kammala kwangilar, kan kudi Naira bilyan 49.6. Duk da hakan babu wani abinda ke nuna akwai wani ci gaba

Binciken da aka yi ya nuna cewa matsalar lamarin kudin kwangilar yana da nasaba ne da yadda dala take kara tin tsada, da sauran wasu abubuwa, ya sa abinda ya hadu da matsala ga gwamnatocin da suka gabata, su sake zama da ‘yan kwangila domin a kammala aikin.

Kafin ya mika wa Shugaban kasa Bola Tinubu mulki, tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari ta amince da amsar aikin da kuma samar da kudadi da hukumar kula da ilimin manyan makarantu (TETFUND).

Lokacin da Ministan ilimi Farfesa Tahir Mamman ya fara aiki a matsayin Ministan ilimi a shekarar 2023, ya yi alkawarin zai ci gaba da kuma kammala aikin nan da shekara ta 2025.

Mamman ya ba da tabbacin cewar dan kwangilar da yake aikin zai dawo wurin, domin ya kammala aikin.

Ya ce“Wannan aikin yana da matukar amfani ga Nijeriya, ga shi kuma ba a kammala shi ba abin ya kusa shekara 20. Mun san muhimmancin dakin karatu, ba wa ma maganar dakin karatu na kasa ba. Don haka matakin da ya dace duk wanda yake da abinda zai yi dangane da wannan aiki, to ya dawo wurin aiki.

“Akwai matsaloli nan da can, amma za a kammala aikin cikin kusan wata 21. Muna yin kira da kamfanin da aka ba kwangilar, ya kammala aikin, saboda aikin ya dauki lokaci mai tsawo, don haka aiki irin wannan bai kamata ayi ta tafiyar Hawainiya ba.

“Don haka koma menene matsalar aikin, mun dauki niyyar kammala shi kamar yadda Ministan ya furta shekara daya data gabata.

Sai dai kuma wakilinmu wanda ya ziyarci wurin bada dadewa ba ya gano bai lura da wata alama ba ko alamun da za su nuna ana samun cigaba ba dangane da aikin dakin karatu, yayin da ziyarar da aka kai wurin da ake aikin ba wani abinda zai burge wanda ya je wurin.

Wannan aikin da aka fara ba a kammala ba ya jawo maganganu daban-daban daga dalibai, masu hrakar koyar da dalibai, inda suke kiran daukar mataki ba da dadewa ba, domin kammala shi saboda ya amfani al’ummar yanzu tare da wadanda za su kasance nan gaba.

A hirar da suka yi da LEADERSHIP, daliban Nijeriya a karkashin inuwar kungiyar dalibai ta kasa (NANS) da masu ruwa da tsaki daban- daban sun yi kira da a dauki matakin gaggawa domin a kammala ginin dakin karatu na kasa domin kuwa aikin ya dade ba a kammala gina shi ba.Ta nuna rashin jin dadinta akan cewar aikin ya tsaya shekaraIt 18 duk kuwa da yake gwamna tocin da suka shude sun yi alkawarin yin hakan.

Da yake furta albarkacin bakinsa jami’in hulda da jama’a na kungiyar Komrade Gundu Mimidoo Joy yace da aikin kowa yana yi ma shi Kallon wuri ne da zai amfani al’ummar Nijeriya musamman ma wadanda su masana ilimi ne, amma yanzu ya kasance wani wurin da aka yi watsi da shi ba tare dayin la’akarin ci bayan ilimi bane ba.

“Dalibai na yi ma shi aikin wani abu da yake da muhimmanci wajen cigaban lamarin koyarwa domin,a samu ilimi mai inganci.Dakatar da shi abin ya wakilci gazawar gwamnati ta ba ilimi kulawar data kamata.Shi yasa wannan tsayawar aikin ya kara bada gudunmawa ta bangaren lalacewar ko rashin ingancin yadda makarantu suke a fadin tarayyar Nijeriya.

Kwangila
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
Next Post
An Kashe Dalibai 3, An Raunata Wani A Harin Da Boko Haram Ta Kai Makarantar ‘Yan Shi’a A Yobe

An Kashe Dalibai 3, An Raunata Wani A Harin Da Boko Haram Ta Kai Makarantar 'Yan Shi'a A Yobe

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.