• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

by Rabi'at Sidi Bala
3 months ago
in Nishadi
0
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban da ga shahararren jarumin fina-finan Hausa Rabilu Musa Ibro, wanda Allah ya yi wa rasuwa shekaru 9 da suka gabata, Hanafi Rabilu Musa Ibro ya bayyana yadda har yanzu suke amfanuwa da zaman arziki da mahaifinsu ya yi da mutane a lokacin da yake raye, Hanafi wanda shima ya shiga harkar barkwanci ya kuma bayyana cewar duk da cewar mahaifin nasu ya dade da rasuwa amma har yanzu mutane suna ci gaba da yi masa addu’oin samun rahamar Ubangiji.

Hanafi a wata hira da ya yi da BBC Hausa ya ce sau da dama a kan kirashi a wata harkar samun kudi kokuma a yi mashi alheri sai ace wannan abin da muka yi maka saboda mahaifinka ne,  a lokuta da dama mu kan ji ko kuma a fada mana cewar mahaifinmu ya samu kyakkyawan yabo a wajen mutanen da ya yi mu’amala dasu da kuma wadanda yake sakawa nishadi, a farkon rayuwata ban sa ran zan yi wani aiki na fim ba.

  • Jajircewa Ce Sirrin Samun Daukakata A Masana’antar Kannywood -Sadik Sani Sadik
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi

Amma bayan rasuwar mahaifina sai naga mutane na ta yabonsa su na yi mashi shaidar ayyukan alheri, sai na yanke shawarar tsunduma harkar ka’in da na’in don kuwa mu an mutu an bar mana gadon abin alheri, duk yanda mutum ke ji da gadon da aka bar mashi a gida nima haka nike jin wannan gadon sana’a da mahaifina ya rasu ya bar mani inji Hanafi.

Hakan kuma yana matukar yi mana dadi, domin babu abinda yafi a yi wa wani naka fatan alheri ko bayan ransa in ji Hanafi, yanzu haka nine Kansila na Wucin Gadi a gundumar Danlasan da ke Qaramar Hukumar Warawa da ke nan Jihar Kano kuma ni dalibi ne a FCE Kano inda nike karatun B.Ed amma nikan samu saukin yin wasu al’amuran sakamakon yadda wasu ke taimakona ta sanadiyar mahaifina inji shi.

Ya kuma kara da cewa har yanzu mu da muke ‘ya’yansa mukan samu wata alfarma a sanadiyarsa, domin a wasu lokutan akwai wuraren da ban kai in shiga wajen ba, amma saboda kasancewata dansa sai a barni in shiga ba tare da wani shinge ko kyara ba, hakan ya sa muke matukar godiya da yadda mutane ke saka shi a cikin addu’oinsu a kowane lokaci, kuna muna fatan Allah SWA ya kyautata makwancinsa.

Labarai Masu Nasaba

Samun KuÉ—i Ya Fi Samun ÆŠaukaka Wahala A Kannywood -Baba SadiÆ™

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IbroKannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Next Post

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Related

Samun KuÉ—i Ya Fi Samun ÆŠaukaka Wahala A Kannywood -Baba SadiÆ™
Nishadi

Samun KuÉ—i Ya Fi Samun ÆŠaukaka Wahala A Kannywood -Baba SadiÆ™

1 day ago
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami
Nishadi

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

1 day ago
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa
Nishadi

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

1 week ago
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa
Nishadi

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

3 weeks ago
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Nishadi

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

4 weeks ago
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

4 weeks ago
Next Post
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 

August 4, 2025
Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

Xi Jinping Ya Ba Da Muhimmin Umarnin Jin Ra’ayoyin Masu Amfani Da Intanet Kan Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-Biyar Na 15

August 4, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

Gwamnatin Tarayya Ta Kwato ₦21bn, Ta Kashe Ƴan Ta’adda 78 — DG NOA

August 4, 2025
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

August 4, 2025
Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

Kwamitin Bincike Ya Miƙa Rahoto Kan Kwamishinan Sufuri Ga Gwamnatin Kano

August 4, 2025
Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

Ruwan Wuta Ne Kawai Maganin ‘Yan Ta’adda Ba Sasanci Ba – Mataimakin Gwamnan Zamfara

August 4, 2025
Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

Gwamna Buni Ya Bukaci Sabon Sarkin Gudi Ya Jagoranci Zaman Lafiya, Hadin Kai, Da Ci Gaban Kasa

August 4, 2025
Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule

August 4, 2025
Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

Tsohon Dan Majalisar Taraba Usman Ya Fice Daga APC

August 4, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane Da Dama A Kauyukan Zamfara

August 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.