• English
  • Business News
Monday, June 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

by Rabi'at Sidi Bala
3 weeks ago
in Nishadi
0
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban da ga shahararren jarumin fina-finan Hausa Rabilu Musa Ibro, wanda Allah ya yi wa rasuwa shekaru 9 da suka gabata, Hanafi Rabilu Musa Ibro ya bayyana yadda har yanzu suke amfanuwa da zaman arziki da mahaifinsu ya yi da mutane a lokacin da yake raye, Hanafi wanda shima ya shiga harkar barkwanci ya kuma bayyana cewar duk da cewar mahaifin nasu ya dade da rasuwa amma har yanzu mutane suna ci gaba da yi masa addu’oin samun rahamar Ubangiji.

Hanafi a wata hira da ya yi da BBC Hausa ya ce sau da dama a kan kirashi a wata harkar samun kudi kokuma a yi mashi alheri sai ace wannan abin da muka yi maka saboda mahaifinka ne,  a lokuta da dama mu kan ji ko kuma a fada mana cewar mahaifinmu ya samu kyakkyawan yabo a wajen mutanen da ya yi mu’amala dasu da kuma wadanda yake sakawa nishadi, a farkon rayuwata ban sa ran zan yi wani aiki na fim ba.

  • Jajircewa Ce Sirrin Samun Daukakata A Masana’antar Kannywood -Sadik Sani Sadik
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi

Amma bayan rasuwar mahaifina sai naga mutane na ta yabonsa su na yi mashi shaidar ayyukan alheri, sai na yanke shawarar tsunduma harkar ka’in da na’in don kuwa mu an mutu an bar mana gadon abin alheri, duk yanda mutum ke ji da gadon da aka bar mashi a gida nima haka nike jin wannan gadon sana’a da mahaifina ya rasu ya bar mani inji Hanafi.

Hakan kuma yana matukar yi mana dadi, domin babu abinda yafi a yi wa wani naka fatan alheri ko bayan ransa in ji Hanafi, yanzu haka nine Kansila na Wucin Gadi a gundumar Danlasan da ke Qaramar Hukumar Warawa da ke nan Jihar Kano kuma ni dalibi ne a FCE Kano inda nike karatun B.Ed amma nikan samu saukin yin wasu al’amuran sakamakon yadda wasu ke taimakona ta sanadiyar mahaifina inji shi.

Ya kuma kara da cewa har yanzu mu da muke ‘ya’yansa mukan samu wata alfarma a sanadiyarsa, domin a wasu lokutan akwai wuraren da ban kai in shiga wajen ba, amma saboda kasancewata dansa sai a barni in shiga ba tare da wani shinge ko kyara ba, hakan ya sa muke matukar godiya da yadda mutane ke saka shi a cikin addu’oinsu a kowane lokaci, kuna muna fatan Allah SWA ya kyautata makwancinsa.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IbroKannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Next Post

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

20 hours ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

1 week ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

2 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

2 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

3 weeks ago
Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe
Nishadi

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

4 weeks ago
Next Post
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Maida Martani Game Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka Kan Kasar Sin

June 1, 2025
Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

Tsohon Minista Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Nasarawa

June 1, 2025
Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

Ranar Yara Ta Duniya: Yadda Shugaba Xi Ya Kasance Tare Da Yara

June 1, 2025
Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

Sin Na Matukar Adawa Da Munanan Kalaman Sakataren Tsaron Amurka

June 1, 2025
Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano

June 1, 2025
Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.