ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

by Rabi'at Sidi Bala
11 months ago
Adam

Ta A ranar ashirin da shida ga watan satumba, shekara ta dubu biyu da ashirin da biyar (26/9/2025). Aka gudanar da bikin nadin sarautar da aka yi wa Haj. Zahra’u Sale Fantami, wacce aka fi sani da Adaman Kamaye cikin shirin Dadin kowa. Ita dai wannan sarauta an gudanar da bikin nadinta a kasar Ghana, inda jama’a ke ta rade-radi game da sarautar. Jarumar ta bayyanawa masu karatu gaskiyar magana game da wannan batu.

Ga dai tattaunawar tare da wakiliyar Jaridar Leadership Hausa RABI’AT SIDI BALA Kamar haka:

  • Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
  • MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

Da farko za ki fadawa masu karatu cikakken sunanki.

ADVERTISEMENT

Sunana Zahra’u Sale Fantami, wacce aka fi sani da Adaman Kamaye ko Adaman Na Ta’ala a cikin shirin Dadin Kowa.

 

LABARAI MASU NASABA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

Ana ta rade-radin an baki sarauta, shin mene ne gaskiyar maganar?

Alhamdulillah, maganar an bawa Zahra’u sarauta ba karya ba ne, hakkun haka ne an ba ni sarauta.

 

Mutane za su so su ji, shin daman Haj. Zahra’u ‘yar Ghana ce, tana da sarauta a Ghana?

A’a! Ni ba ‘yar Ghana ba ce, ba abin da na hada da Ghana, sai dai so da yarda, saboda ma’abota kallon finafinan hausa ne. Ni kuma ina cikin wannan masana’anta ta finafinan hausa, musamman Dadin Kowa na Arewa24. Alhamdulillah Arewa24 ta sa sunanmu ya tafi a duniya. Ta yi mana riga ta yi mana wando babu abin da ba ta yi mana ba, domin dalilin fuskanmu da ta tafi ake kaunar mu har ake karrama mu.

 

Me ya sa aka baki sarauta?

An ba ni wannan sarauta ne ba dan na gada ba, an ba ni ne a matsayin cancanta, da so da yarda da amincewa a birnin Kumasi da Accra. Na ziyarci wadannan masarautu domin karrama su da basu allon girma wato ‘Award’. Na je na gaishe su, na ziyarce su, ubangiji Allah ya sa suka ce da ni to, wannan sarki na Kumasi ya ce da ni,shi fa ba zai iya yi min komai ba sai dai ya ba ni Jakadiyarsa ta London da America, da nan Kumasi da kuma Najeriya. Haka zalika shi kuma sarkin Accra ya ba ni magajiyarsa ta London da America da Accra da kuma nan Najeriya. Alhamdulillah kuma na gode, an karrama ni kuma na ji dadi.

 

Me ya fi burge ki a nadin sarautar da aka yi miki?

To, Alhamdulillah ita dai wannan sarauta, sarauta ce me dadi, an ba ni kudi sannan kuma an yi min albashi. Sannan ga alfarma, alfarmar da aka yi min idan za a fita kamar turai wajen London zuwa America an ba ni alfarmar mutum uku ni ta hudu. Za a ba ni kujera mu je mu dawo duk abin da za a yi. Sannan alfarma ta biyu idan a Ghana za a yi taro an ba ni alfarmar mutum goma sha daya ni ta sha biyu, za a ba ni kujera mu je mu dawo. Dan haka wannan abun alfahari ne a gare ni.

 

Wane irin farin ciki ki ke ji game da wannan sarauta da aka baki?

Gaskiya na ji dadi kwarai da gaske, kuma na yi wa Allah godiya. Dan ban taba tsammanin zan taka wannan mataki ba, wanda Allah ya sa ina da rabon shi. Kuma na taka shi, komai nufin Allah ne. Mutanen Ghana sun nunan tamkar uwa daya uba daya, an karramani an mutuntani an daukake ni, ina alfahari da mutanen Ghana, sun ba ni tarihin da ba zan taba mantawa da shi a rayuwata ba.

 

Ko akwai wani abu da ki ke son fada wanda baki fade shi ba, game da wannan sarauta?

Ina mika sakon godiya musamman ga mai girma Alh. Ahmed Ibrahim Watara, shi ne sarkin Wangarawan Kumasi Allah ya kara masa lafiya, shi ya fara ba ni wannan mikami na Jakadiya. Shi kuma Alhaji Yahaya Hamisu Bako maimartaba (Sarkin Zangon Accra), Ghana shi kuma ya ba ni magajiya. Ina mika godiya ta musamman ga Alh. Armaya’u Sulaiman (Sarkin Daddawan Ablekuma Central), sannan shugaban matasan Bilbila. Ina mika godiya ta musamman ga sauran mukarraban fada bakidaya, ba zan iya cewa sai na kira sunan kowa da kowa ba, amma a gurguje akwai Haj. Fati Sarauniya (Sarauniyar Zangon Accra), akwai Haj. Hauwa (Majidadiyar Accra, akwai Haj. Magajiya (Magajiyar Zangon Accra), akwai Haj. Gado (Wakiliyar Bare-bari), akwai Hajiya magajiya (Wakiliyar Wangarawa), Akwai Uncle Sonihi (Sarkin Jaddada zaman lafiya na Wangarawa), Da Dan’masani (Wangarawa). Ina mika godiya ga dukkanin mukarraban wannan fada masu daraja, Alhamdulillah Ala kulli hal, ina yi wa kowa fatan alkhairi.

 

Me za ki ce ga masoyanki?

Ina son masoyana na fadin duniya su tayani addu’a da fatan alkhairi, da fatan Allah ya sa mu gama lafiya. Ina kira ga masoyana idan an ga zan yi abin da ba daidai ba a biyo ta social media a sanar da ni, domin in gyara. In an ga zan yi kuskure a bani shawara ta kafafen sadarwa, inda sako zai same ni cikin sauki. Makiya kuma ina so su kara sako ido saboda sai da gishirinsu muke samun suga, a fuskar makiyi muke gane aikin mu ya yi kyau ko bai ba. Allah ya karo mana dubun makiya dan mu ba ma so su yi kasa.

Wassalamu Alaikum.

Adam
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Alaƙata Da Adamu Zango Ta Bunƙasa A Kannywood —Jarumi Ibrahim Sodangi 
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

MASU ALAKA

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
Nishadi

Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa

September 5, 2026
Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood
Nishadi

Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

August 29, 2026
Adam
Nishadi

Dalilan Da Suka Sa Ba Zan Iya Auren Ɗan Film Ba —Bilkisu Bishasha

August 23, 2026
Next Post
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.