• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina

by Rabi'u Ali Indabawa
11 months ago
in Tsaro
0
Har Yanzu Garuruwa 24 Na Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara Da Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da hare-haren da sojoji ke ci gaba da kai wa a jihohin Katsina da Zamfara na fatattakar ‘yan ta’adda, har yanzu ‘yan bindiga na ci gaba da mallake al’ummomi da dama a kananan hukumomi 24 na jihohin biyu.

Ayyukan ‘yan bindigar sun fi bayyana a jihar Zamfara inda wasu majiyoyi da ba na hukuma ba suka ce al’ummomin da barayin ke rike da jama’a na karbar kudin fansa sama da 100 a kananan hukumomi 14.

  • Shugaban Sakandare Daga Zamfara Ya Zama Gwarzon Malami Na 2024 A Duk Faɗin Nijeriya 
  • Gwamnatin Katsina Za Ta Bude Shagunan Sayar Da Kayan Masarufi Masu Rahusa

A Jihar Katsina, LEADERSHIP Sunday ta ruwaito cewa, a halin yanzu babu wata majalisa da ke hannun ‘yan bindigar, amma har yanzu suna rike da madafun iko a wasu kananan hukumomi 10.

Wata majiya daga Karamar Hukumar Faskari ta Jihar Katsina ta yi zargin cewa kimanin al’ummomi 32 ne aka yi watsi da su sakamakon hare-haren da ‘yan bindiga suka kai musu. Ya bayyana sunayen al’ummomin da suka hada da Ungwar Dorowa, Ungwar Bika, Gidan Wakili, Kogon Kura, Gidan Saidu, Migyadali da Shuwaki, da sauransu.

A kwanakin baya ne dai Shugaba Bola Tinubu ya umurci Ministan tsaro da babban hafsan tsaro (CDS) da sauran hafsoshin tsaro da su koma Sokoto domin fatattakar ‘yan bindiga daga jihohin Zamfara, Sokoto, Katsina da Zamfara.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

An Cafke Mutum Hudu Bayan ‘Yan Fashi 20 Sun Afka Wasu Gidaje A Bauchi

Tun daga wannan lokacin, sojoji da ‘yan sanda sun kashe manyan shugabannin ‘yan fashi tare da kama wasu da dama.

Amma binciken da LEADERSHIP Sunday ta gudanar a Jihohin Katsina da Zamfara ya nuna cewa har yanzu al’ummomi da dama ba su tsira daga ‘yan fashin ba.

Wani bincike da aka gudanar a Zamfara ya nuna cewa har yanzu galibin al’ummomin daga kananan hukumomi 14 na jihar na hannun ‘yan bindiga duk da harin da sojoji suka kai musu inda aka kashe da dama daga cikinsu ciki har da daya daga cikin manyan sarakunan da ake nema ruwa a jallo, Halilu Sububu.

Wasu mazauna yankin sun ce hare-haren da sojoji suka kai ya kawo raguwar hare-haren, amma a wasu sassan jihar, ‘yan fashin sun bijirewa sojojin ne a yayin da suke fafata yakin.

Al’ummar yankin sun ce abin takaici ne yadda sama da al’ummomi 100 daga sassan kananan hukumomin 14 ba su kubuta daga hare-haren ‘yan bindiga da cin zarafi ba.

Sun ce yayin da aka tilastawa wasu daga cikin mutanen kauyen gudun hijira zuwa birane saboda fargabar ci gaba da kai hare-hare, wasu da suka zabi zama a baya an tilasta musu zama a karkashin umarnin miyagun.

Wakilinmu ya gano cewa kauyukan da aka fi fama da wadannan miyagu su ne a kananan hukumomin Maru, Anka, Shinkafi, Maradun, Zurmi, Gusau da Bungudu.

A Karamar Hukumar Zurmi, kauyukan da ake zargin na hannun ‘yan ta’addar sun hada da Gidan Kabbo, Tsakauna, Dogon-hako, Gidan duwan, Jididi, Asako, Gidan-Oho, Dunnu, Gwamawa, Gidan Labbobuzu, Marmaro, Takalmawa, Tukurawa, Sangamawa, Tataka. Gidan-Galadima, Gidan-Zago, Kadamutsa, Holuwa, Makosa, Judidi, Geza, Rinni da Dadan.

A Karamar Hukumar Tsafe, kauyukan da lamarin ya shafa sun hada da Munhaye, Dustin Kura, Kekawa, Yarzaiga, Sabon Birnin Nakak, Unguwar Gyauro, Matso-Matso, Magazawa, Kawasaki, Bare-Bari, Turba-Kuceheri, Marne, Maidagalo, Yar-tsakuwa. Garkuwan, Kofar Fasa, Sansami and Dankutau.

A Karamar Hukumar Maru, kauyukan da ke karkashin ikon ‘yan bindiga sun hada da Madada, Bingi, Dandalla, Babbar Doka, Kabaro, Sangeku, Danmani, Kunjemi, Karauci, Gajeran Kauye, Saulawa, Randa, Kango, Balge, Gobirawan Cali, Gidan Ardo, Bulakke da Kilin.

A majalissar Anka, kauyukan da rikicin ya shafa sun hada da Rafin Sanya, Barayar Zaki, Rafin Gero, Karfa, Bawar Daji, Sunka, Tungar Kudaku, Matseri, Dankalgo, Matsafa, Nassarawa da Kawaye.

A karamar hukumar Maradun, al’ummar sun hada da Aljimma, Gwargawo, Kuzi, Ruwan Bado, Magamin Diddi, Gareka, Saurar Kade, Damage, Asarara, Burmi Gidan Adamu, Gidan Maidawa, Gidan Baushi, da Wari.

A karamar hukumar Talata Mafara, Ruwan Jema, Ruwan Gora, Dankalgo, da Ruwan Gizi suna fama da wannan kaddara.

A karamar hukumar Gusau, kauyukan da ‘yan bindigar ke hannun ‘yan fashin sun hada da Madaro, Kungurmi, Dandindin, Burwaye, Burnai, Fankarfe, Dadin Zama, Bakin Dutse, Tungar Kudi, Ruwan Mesa, Koli, Buzaye, Lilo, Tungar Rakumi, Rijiya, da Kwarya Tsugune. .

A Karamar Hukumar Birnin Magaji, kauyukan sun hada da Madomawa, Nasarawa Mailayi, Dan’Ali, Birnin Tsaba, da sauransu.

Da yake zantawa da LEADERSHIP Sunday, Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamna (SSA) kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a Mustapha Jafaru, ya ce Gwamna Dauda Lawal ya tabbatar wa jama’a cewa gwamnatinsa za ta yi duk mai yiwuwa ga dan’Adam wajen ganin an samu zaman lafiya gaba daya a jihar.

Mataimakin ya ce gwamnan ya yi isassun shirye-shirye da jami’an tsaro domin duba yadda ‘yan bindigar suka wuce gona da iri da kuma ceto mutanen kauyen daga hannunsu.

Ya ce gwamnatin Gwamna Lawal ba ta da wani shiri na sasantawa da ‘yan bindigar ko tattaunawa da su ba tare da la’akari da ayyukansu ba.

“Gwamnatin jihar za ta fuskance su gaba daya ta kuma yi maganinsu domin a dawo da tsaro da yardar Allah,” in ji Kaura.

Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Yazeed Abubakar, ya ce ‘yan sanda tare da hadin gwiwar sauran jami’an tsaro suna yin duk mai yiwuwa wajen ganin an kwato yankunan da ake zargin suna karkashin ikon ‘yan bindiga.

Kakakin Rundunar 1 Brigade na Rundunar Sojan Nijeriya (OPHD), Gusau, Laftanar Sulaiman Omale, ya ce ba zai ce uffan ba kan duk wani batu da ya shafi tsaro domin ba a umurce shi ya yi magana ba.

A jihar Katsina, yankunan da ‘yan ta’addan ke addabar sun hada da Faskari, Sabuwa, Safana, Kankara, Dutsin-ma, Danmusa, Jibia, Batsari, Kurfi, da Dandume.

A garin Faskari wasu al’ummomi irinsu Kadisau, Fankama, da Sabon Layin Galadima sun koma tattaunawa da ‘yan fashin tare da biyan kudaden haraji domin shiga gonakinsu.

Duk da haka, wasu irin su Jarkuka, Ungwan Sakkai da Kampani na ci gaba da fuskantar barazana.

A Karamar Hukumar Batsari, al’ummomi irinsu Batsari Anabi, Garin Yara da Dan Kwalaso na fuskantar irin wannan kalubale.

A Karamar Hukumar Kankara, yankin Fanwa da Mabai suna da hatsarin gaske yayin da Marke, Domawa, Maidabino da Dan Ali a Karamar Hukumar Danmusa aka gano a matsayin al’ummomi masu hadari da ‘yan fashi ke kai wa.

Wani babban jami’in gwamnati da ya nemi a sakaya sunansa ya tabbatar da cewa an samu raguwar masu aikata laifuka sosai biyo bayan tura karin jami’an tsaro a yankin.

Kakakin Rundunar ’Yan sandan Jihar Katsina, Sadik Abubakar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArmyKatsinaTsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nazari A Kan Tsare-tsaren Aikin Noma Na Nijeriya Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

Next Post

Shin Dawowar Ahmad Musa Za Ta Taimaka Wa Kano Pillars?

Related

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Tsaro

‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

1 week ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Tsaro

An Cafke Mutum Hudu Bayan ‘Yan Fashi 20 Sun Afka Wasu Gidaje A Bauchi

1 week ago
NDLEA Ta Kama Wani Matashi Dan Shekara 29 Da Kwayoyin Tramadol 7,000 A Kano
Tsaro

NDLEA Ta Kama Wani Matashi Dan Shekara 29 Da Kwayoyin Tramadol 7,000 A Kano

1 week ago
Al’umma Da Ƴan Bindiga Sun Sa Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Katsina
Tsaro

Al’umma Da Ƴan Bindiga Sun Sa Hannu Kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Katsina

1 week ago
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara
Tsaro

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

2 weeks ago
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
Tsaro

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

4 weeks ago
Next Post
Shin Dawowar Ahmad Musa Za Ta Taimaka Wa Kano Pillars?

Shin Dawowar Ahmad Musa Za Ta Taimaka Wa Kano Pillars?

LABARAI MASU NASABA

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.